Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 46:27 - Littafi Mai Tsarki

27 “Ya bawana Yakubu, kada ka ji tsoro, Kada ka firgita, ya Isra'ila. Gama zan cece ka daga ƙasa mai nisa, Zan ceci zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yakubu zai komo, ya yi zamansa da rai kwance, Ba wanda zai razanar da shi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

27 “Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 46:27
24 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kada ku ji tsoro, ina tare da ku! “Daga gabas mafi nisa, da kuma yamma mafi nisa, Zan kawo jama'arku zuwa gida.


Ya Isra'ila, Ubangiji wanda ya halicce ku ya ce, “Kada ku ji tsoro, na fanshe ku. Na kira ku da sunanku, ku nawa ne.


Zan komar da Isra'ila a makiyayarsa, zai yi kiwo a Karmel da Bashan. Zai sami biyan bukatarsa a tsaunukan Ifraimu da na Gileyad.


Za ku same ni, ni Ubangiji na faɗa, zan mayar muku da arzikinku, in tattaro ku daga cikin dukan al'ummai da dukan wurare inda na kora ku, ni Ubangiji na faɗa, zan komo da ku a wurin da na sa a kwashe ku a kai ku zaman talala.’ ”


Zan komo da mutanena ƙasarsu, Za su giggina biranensu da suka rurrushe, Su zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi, su sha ruwan inabin. Za su yi lambuna, su ci amfaninsu.


A waɗannan kwanaki za a ceci mutanen Yahuza, mutanen Urushalima kuwa za su zauna lafiya. Sunan da za su sa wa Urushalima birninsu, shi ne, ‘Adalcinmu Ubangiji ne.’


A zamaninsa za a ceci Yahuza, Isra'ila kuwa za ta zauna lafiya. Sunan da za a kira shi da shi ke nan, ‘Ubangiji Adalcinmu.’


Ni ne Ubangiji wanda ya halicce ku, Tun farko, na taimake ku. Kada ku ji tsoro, ku bayina ne, Zaɓaɓɓun mutanena waɗanda nake ƙaunarsu.


Ga shi, zan tattaro su daga dukan ƙasashe inda na kora su, da fushina, da hasalata, da haushina. Zan komo da su a wannan wuri, zan sa su su zauna lafiya.


“Saboda haka, ni Ubangiji Allah, na ce yanzu zan komo da zuriyar Yakubu daga bauta in nuna mata jinƙai. Zan yi kishi domin sunana mai tsarki.


Zan kwaso ku daga cikin al'ummai, in tattaro ku daga dukan ƙasashe, in kawo ku cikin ƙasarku.


Ubangiji Allah kuwa zai sawwaƙe wa jama'ar Isra'ila azaba da wahala da suke sha, daga kuma aikin da aka tilasta su su yi.


Ubangiji ya ce, “Ka saurara yanzu, ya Isra'ila, bawana, Zaɓaɓɓun mutanena, zuriyar Yakubu,


Kada zuciyarku ta yi suwu, Kada kuma ku ji tsoro saboda labarin da ake ji a ƙasar, Labari na wannan shekara dabam, na wancan kuma dabam, A kan hargitsin da yake a ƙasar, Mai mulki ya tasar wa mai mulki.


Ubangiji ya ce wa Urushalima, “Zan komo da Saduma da Samariya da 'ya'yansu mata daga bauta. Sa'an nan zan komo da ke daga bauta tare da su,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ