Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 46:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan sauran al'umma.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 46:1
13 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ga shi, a wannan rana na ba ka iko a kan al'ummai da mulkoki, Don ka tumɓuke, ka rusar, Ka hallakar, ka kaɓantar, Ka gina, ka dasa.”


Wato Allah, Allahn Yahudawa ne kurum? Ashe, ba na al'ummai ba ne kuma? Hakika na al'ummai ne ma,


Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Bayan ɗaukaka ya aike ni zuwa wurin al'umman duniyan nan da suka washe ku, gama wanda ya taɓe ku, ya taɓi ƙwayar idona.


Zaki ya hauro daga cikin ruƙuƙinsa, Mai hallaka al'ummai ya kama hanya, Ya fito daga wurin zamansa don ya mai da ƙasarku kufai, Ya lalatar da biranenku, su zama kango, ba kowa.


Gama daga kan duwatsu na gan su, Daga bisa kan tuddai na hange su, Jama'a ce wadda take zaune ita kaɗai, Sun sani sun sami albarka fiye da sauran al'ummai.


Daga waɗannan ne mazauna a bakin gāɓa suka yaɗu bisa ga ƙasashensu, kowanne da harshensa, bisa ga iyalansu da kabilansu.


Nebukadnezzar zai zo ya buga ƙasar Masar. Zai ba annoba waɗanda aka ƙaddara su ga annoba, waɗanda aka ƙaddara ga bauta, za a kai su bauta. Waɗanda aka ƙaddara ga takobi, za su mutu ta takobi.


A kan rana ta goma sha biyu ga watan goma a shekara ta goma, sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,


A kan rana ta fari ga watan uku a shekara ta goma sha ɗaya, Ubangiji ya kuma yi magana da ni, ya ce,


A kan rana ta fari, ga watan goma sha biyu, a shekara ta goma sha biyu, sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,


Za su ci gaba da juye tarunsa ke nan? Su yi ta karkashe al'umman duniya ba tausayi?


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ