Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 31:22 - Littafi Mai Tsarki

22 Har yaushe za ki yi ta shakka, Ya ke 'yar marar bangaskiya? Gama Ubangiji ya halitta sabon abu a duniya, Mace ce za ta kāre namiji.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

22 Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya ’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 31:22
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Me ya sa kuke taƙama da ƙarfinku, Ƙarfinku da yake ƙarewa, ku mutane marasa aminci? Kun dogara ga dukiyarku, Kuna cewa, ‘Wane ne zai iya gāba da mu?’


Amma ba su yi biyayya ba, ba su kuma kula ba. Sai suka bi shawarar kansu da ta tattaurar muguwar zuciyarsu. Suka koma baya maimakon su yi gaba.


Za ta haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, domin shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”


Mutanena sun himmantu su rabu da ni, Ko da yake an kira su ga Ubangiji, Ba wanda ya girmama shi.


Ya mutanen Samariya, ina ƙin maraƙinku na siffa. Ina jin haushinsu ƙwarai! Sai yaushe za su rabu da gumaka?


Mutanen Isra'ila masu taurinkai ne kamar alfadari. Ta yaya Ubangiji zai yi kiwonsu Kamar 'ya'yan tumaki a makiyaya mai fāɗi?


Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki, Domin a cece ki, Har yaushe mugayen tunaninki za su yi ta zama a cikinki?


“Ku juyo ku marasa aminci, Zan warkar da rashin amincinku. “To, ga shi, mun zo gare ka, Gama kai ne Ubangiji Allahnmu,


A zamanin sarki Yosiya, Ubangiji ya ce mini, “Ka ga abin da take yi, ita marar amincin nan, wato Isra'ila? Yadda a kowane tudu mai tsayi, da a gindin kowane itace mai duhuwa, a wurare ne ta yi karuwancinta.


Me ya sa ba ku da tsayayyiyar zuciya, Sai ku yi nan ku yi can? Masar za ta kunyata ku kamar yadda Assuriya ta yi.


Ƙaƙa za ka ce ba ka ƙazantar da kanka ba, Ba ka taɓa bin gunkin nan Ba'al ba? Ka duba hanyarka ta zuwa cikin kwari, ka san abin da ka yi. Kana kama da taguwa, mai yawon neman barbara.


Wace riba ka samu, har da ka tafi Masar, Don ka sha ruwan Kogin Nilu? Wace riba ka samu, har da ka tafi Assuriya, Don ka sha ruwan Kogin Yufiretis?


Yanzu fa, Ubangiji kansa zai ba ku alama. Wata budurwa wadda take da ciki, za ta haifi ɗa, za a raɗa masa suna Immanuwel.


Amma idan Ubangiji ya aikata wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara zuwa cikin lahira a raye, sa'an nan za ku sani mutanen nan sun raina Ubangiji.”


Zan sa ƙiyayya tsakaninka da matar, tsakanin zuriyarka da zuriyarta, shi zai ƙuje kanka, kai za ka ƙuje diddigensa.”


“Amma suka ƙi ji, suka ba da baya, suka toshe kunnuwansu don kada su ji.


Ubangiji ya ce, “Zan warkar musu da riddarsu. Zan kuma ƙaunace su sosai, Gama fushina zai huce.


Irmiya ya ce, “Ko da yake zunubanmu su ne shaidunmu, Ya Ubangiji, ka yi taimako saboda sunanka! Gama kāsawarmu ta yi yawa, Domin mun yi maka zunubi.


Na ga abubuwanku masu banƙyama, Wato zinace-zinacenku, da haniniya kamar dawakai, Da muguwar sha'awarku ta karuwanci a kan tuddai da filaye, Ya Urushalima, taki ta ƙare! Har yaushe za a tsarkake ki?”


“Ku komo, ya ku mutane marasa aminci, Gama ni ne Ubangijinku. Zan ɗauki mutum guda daga kowane gari, In ɗauki mutum biyu daga kowane iyali, Zan komo da su zuwa Dutsen Sihiyona.


Amma da lokaci ya yi sosai, sai Allah ya aiko Ɗansa, haifaffen mace, haifaffe kuma a ƙarƙashin Shari'a,


Yahuza kuwa ta ga dukan karuwancin da marar amincin nan, Isra'ila ta yi, na sake ta, na ba ta takardar sarki. Amma duk da haka maƙaryaciyar 'yar'uwan nan tata, Yahuza, ba ta ji tsoro ba, amma ita ma ta tafi ta yi karuwanci.


Ubangiji ya ce, “Idan mutum ya saki matarsa, Ta kuwa rabu da shi, har ta auri wani, Ya iya ya komo da ita? Ashe, yin haka ba zai ƙazantar da ƙasar ba? Ya Isra'ila, kin yi karuwanci, Abokan sha'anin karuwancinki, suna da yawa. Za ki sāke komowa wurina? Ni, Ubangiji, na faɗa.


“Yanzu kin ce, ‘Kai ne mahaifina, Ka ƙaunace ni tun ina cikin ƙuruciyata.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ