Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 22:6 - Littafi Mai Tsarki

6 Abin da Ubangiji ya ce ke nan a kan fādar Sarkin Yahuza, “Kyanta kamar Gileyad take a gare ni, Kamar kuma ƙwanƙolin Lebanon. Duk da haka zan maishe ta hamada, Birnin da ba kowa ciki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

6 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 22:6
26 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Na yi tambaya na ce, “Har yaushe zai ta zama haka, ya Ubangiji?” Sai ya amsa, ya ce, “Har birane suka zama kufai ba kowa ciki. Har gidaje suka zama kangwaye. Har ƙasar kanta ta zama ba kowa, marar amfani.


Ya mai da ƙasa mai dausayi ta zama mai gishiri, marar amfani, Saboda muguntar waɗanda suke zaune a can.


Saboda ku kuwa za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za ta zama tsibin kufai, Dutse inda Haikali yake zai zama kurmi.


Birni mai garu ya zama kufai. An bar shi kamar jejin da ba kowa ciki. Ya zama wurin kiwon shanu, inda za su huta su yi kiwo.


“Mika kuwa, mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya, Sarkin Yahuza, ya faɗa wa dukan mutanen Yahuza cewa, “ ‘Ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce, Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za ta zama tsibin juji, Ƙwanƙolin dutsen Haikalin zai zama kurmi.’


“Ni Ubangiji na ce, zan mai da Urushalima tsibin kufai, Wurin zaman diloli, Zan kuma mai da biranen Yahuza kufai, inda ba kowa.”


Zan sa muryar murna da ta farin ciki, da muryar ango da ta amarya su ƙare a biranen Yahuza da titunan Urushalima, gama ƙasar za ta zama kufai.”


Suka zauna su ci abinci, da suka ɗaga ido suka duba, sai ga ayarin Isma'ilawa suna zuwa daga Gileyad, da raƙumansu ɗauke da ƙāro, da man ƙanshi na wartsakewa, da mur, suna gangarawa kan hanyarsu zuwa Masar.


“Ni Ubangiji na rantse da raina, ko da Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, zoben hatimi ne a yatsan hannun damana, duk da haka zan kwaɓe shi,


Zan hukunta ku bisa ga ayyukanku,’ in ji Ubangiji, ‘Zan sa wa jejin ƙasar wuta. Za ta cinye duk abin da yake kewaye da ita.’ ”


Are we “Sai ka faɗa wa gidan sarautar Yahuza cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji,


Bala'i a kan bala'i, Ƙasa duka ta zama kufai, An lalatar da alfarwaina, ba zato ba tsammani, Labulena kuwa farat ɗaya.


Cinyoyinsa kamar ginshiƙan da aka yi da dutsen alabasta, Aka kafa su a cikin kwasfar zinariya. Kamanninsa kamar Dutsen Lebanon ne, Da itatuwan al'ul ɗinsa mafi kyau.


Ka yarje mini, ina roƙonka in haye in ga wannan kyakkyawar ƙasa a hayin Urdun, ƙasan nan mai kyau ta tuddai, da Lebanon.’


Kabilan Ra'ubainu da Gad suna da dabbobi da yawa ƙwarai. Da suka ga ƙasar Yazar da ta Gileyad wuri ne mai kyau domin shanu,


Kyakkyawa ce ke ƙaunatacciyata. Idonki kamar na kurciya, suna haskakawa daga cikin lulluɓi. Gashinki yana zarya kamar garken awaki Da yake gangarowa daga tuddan Gileyad.


Domin haka za a kunyatar da Babila sosai, inda kuka fito. Za ta zama ta baya duka a cikin sauran al'umma, Za ta zama hamada, busasshiyar ƙasa.


Ki buɗe ƙofofinki, ke Lebanon, Don wuta ta cinye itatuwan al'ul naki.


Ka aike da barorinka don su yi mini fāriya, da cewa ka ci nasara da duwatsu mafi tsayi da karusanka, har da ƙwanƙolin Dutsen Lebanon. Kana fāriya da cewa a can ka sare dogayen itatuwan al'ul da na fir, ka kuma kai wuri mafi nisa na jeji.


Zaki ya hauro daga cikin ruƙuƙinsa, Mai hallaka al'ummai ya kama hanya, Ya fito daga wurin zamansa don ya mai da ƙasarku kufai, Ya lalatar da biranenku, su zama kango, ba kowa.


Ba abin sanyayawa a Gileyad ne? Ba mai magani a can ne? Me ya sa ba a warkar da jama'ata ba?


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ