Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 2:32 - Littafi Mai Tsarki

32 Budurwa ta manta da kayan kwalliyarta? Ko kuwa amarya ta manta da kayan adonta? Amma mutanena sun manta da ni kwanaki ba iyaka.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

32 Budurwa za tă manta da kayan adonta amarya ta manta da kayan adon aurenta? Duk da haka mutanena sun manta da ni, kwanaki ba iyaka.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 2:32
24 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Suka manta da Allah wanda ya cece su, Ta wurin manyan ayyuka da ya yi a Masar.


Ubangiji ya ce, “Wannan shi ne rabonku, Rabon da na auna muku, ni Ubangiji na faɗa. Domin kun manta da ni, kun dogara ga ƙarairayi,


An ji murya a kan filayen tuddai, Kūka da roƙo ne na 'ya'yan Isra'ila maza, Domin sun rabu da hanyarsu, Sun manta da Ubangiji Allahnsu.


Akwai wata al'umma da ta taɓa sāke gumakanta Ko da yake su ba kome ba ne? Amma mutanena sun sauya darajarsu da abin da ba shi da rai.


Isra'ila, kin manta da Allah wanda ya kuɓutar da ke, wanda ya kāre ki kamar babban dutse. Kin dasa wa kanki lambuna masu ni'ima don ki yi wa gumaka sujada.


“Gama mutanen Isra'ila sun manta da Mahaliccinsu, Sai sun gina manyan gidaje masu daraja. Mutanen Yahuza kuma sun yawaita biranensu masu garu, Amma ni Ubangiji, zan aika da wuta a kan biranensu, Ta ƙone fādodinsu.”


Urushalima tana murna saboda abin da Ubangiji ya yi. Tana kama da amaryar da ta sha ado a ranar aurenta. Allah ya suturce ta da ceto da nasara.


Mutuwa ce maƙarar dukan mugaye, Da dukan waɗanda suke ƙin Allah.


Amma mutanena sun manta da ni, Sun ƙona wa gumaka turare. Sun yi tuntuɓe a cikin al'amuransu, a hanyoyin dā, Sun bi ɓarayin hanyoyi, ba su bi karauka ba.


Wannan muguwar jama'a, wadda ta ƙi jin maganata, wadda ta taurare, ta bi son zuciyarta, ta kuma bi gumaka ta bauta musu, ta yi musu sujada, za ta zama kamar abin ɗamaran nan, wanda ba shi da sauran amfani.


Sai na ga tsattsarkan birni kuma, Sabuwar Urushalima, tana saukowa daga Sama daga wurin Allah, shiryayyiya kamar amaryar da ta yi ado saboda mijinta.


A cikinka mutane suka karɓi toshi don su zub da jini. Kana ba da rance da ruwa da ƙari, kana kuma cin riba a kan maƙwabcinka saboda cutar da kake yi masa, ka kuwa manta da ni, ni Ubangiji na faɗa.


Sa'ad da raƙuman suka gama sha, mutumin ya ɗauki zoben zinariya mai nauyin rabin shekel, ya sa mata a hanci. Ya kuma ɗauki mundaye biyu na shekel goma na zinariya ya sa a hannuwanta,


“Ku 'yan matan Isra'ila, ku yi makoki domin Saul! Ya suturta ku da mulufi mai ƙayatarwa, Ya yi muku adon lu'ulu'u da zinariya.


Sai baran ya kawo kayan ado na azurfa, da na zinariya, da tufafi, ya bai wa Rifkatu, ya kuma ba ɗan'uwanta da mahaifiyarta kayan ado masu tsada.


Sa'ad da ya ga zoben da mundaye da suke hannuwan 'yar'uwarsa, sa'ad da kuma ya ji maganar Rifkatu 'yar'uwarsa cewa, “Ga abin da mutumin ya faɗa mini,” sai ya je wurin. Ya kuwa same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.


Ubangiji ya ce, “Wa ya sa ku fargaba, kuke jin tsoronsa, har kuka yi ƙarya? Ba ku tuna da ni, ko ku kula da ni ba? Ashe, ban yi haƙuri tun da daɗewan nan ba, duk da haka kuwa ba ku ji tsorona ba?


Kun sani sarai yadda za ku yi ku farauci masoya, Har mugayen mata ma, kun koya musu hanyoyinku.


“Yeshurun ya yi ƙiba, yana harbin iska, Ka yi ƙiba, ka yi kauri, ka yi sumul. Ya rabu da Allahn da ya yi shi, Ya raina Dutsen Cetonsa.


Suka daina bauta wa Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga magabtan da suke kewaye da su.


Suna zaton za su sa mutanena su manta da sunana ta wurin mafarkansu da suke faɗa wa junansu, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana saboda Ba'al.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ