Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 17:18 - Littafi Mai Tsarki

18 Bari waɗanda suka tsananta mini su sha kunya, Amma kada ka bar ni in kunyata. Bari su tsorata, Amma kada ka bar ni in tsorata. Ka aukar musu da ranar masifa, Ka hallaka su riɓi biyu!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

18 Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 17:18
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ka sa a kori waɗanda suke ƙoƙari su kashe ni, a kunyatar da su! Ka sa waɗanda suke mini maƙarƙashiya su juya da baya, su ruɗe!


Amma Ubangiji kana tare da ni Kamar jarumi mai bantsoro, Don haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe, Ba za su rinjaye ni ba. Za su sha kunya ƙwarai, Gama ba za su yi nasara ba. Ba za a manta da su ba.


Amma ya Ubangiji Mai Runduna, mai shari'ar adalci, Kakan gwada zuciya da tunani, Ka yarda mini in ga sakayyar da za ka yi mini a kansu, Gama a gare ka na danƙa maganata.


Ka sa masu so su kashe ni, A ci nasara a kansu, su ruɗe! Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina Su koma baya, su sha kunya!


Amma kafin su farga, hallaka za ta kama su. Tarkunan da suka kafa za su kama su, Su kuma fāɗa cikin ramin da suka haƙa!


Ku saka mata daidai da yadda ta yi, Ku biya ta ninkin ayyukanta, Ku dama mata biyun abin da ta dama muku.


Amma ni ban yi gudun zaman makiyayi a gabanka ba, Ban kuma so zuwan ranar bala'i ba, Ka kuwa sani. Abin da ya fito daga bakina kuwa, A bayyane yake gare ka.


Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, abin gādona kuma sun cika shi da abubuwansu na banƙyama.”


A gare ka, ya Ubangiji, lafiya lau nake, Faufau kada ka bari a yi nasara da ni!


Ka sa masu so su kashe ni, A ci nasara a kansu, su ruɗe! Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina, su koma baya, su sha kunya!


Ya yi ta yi mini rauni a kai a kai, Ya fāɗa mini kamar soja da ƙiyayya ta haukata.


“Irmiya, ka faɗa wa mutanen baƙin ciki da ya same ka, Ka ce, ‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana, Kada su daina, saboda an buge budurwa, 'yar jama'ata, An yi mata babban rauni da dūka mai tsanani.


Amma kai, ka tashi ka sha ɗamara, ka faɗa musu dukan abin da na umarce ka. Kada ka ji tsoronsu domin kada in tsoratar da kai a gabansu.


Amma kai, ya Ubangiji, kana sane da ni, kana ganina, Kai kanka kake gwada tunanina. Ka jawo su kamar tumaki zuwa mayanka, Ka ware su domin ranar yanka.


Ya Ubangiji, begen Isra'ila, Duk waɗanda suka rabu da kai, za su sha kunya. Waɗanda suka ba ka baya a duniya za a rubuta su Domin sun rabu da Ubangiji, maɓuɓɓugar ruwan rai.


Haka Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi ka tsaya a ƙofar Biliyaminu, wadda sarakunan Yahuza suke shiga da fita ta cikinta, ka kuma tafi dukan ƙofofin Urushalima.


Ya Ubangiji ka inganta jaruntakarsu, Ka karɓi aikin hannuwansu, Ka murƙushe ƙarfin abokan gābansu, Da waɗanda suke ƙinsu don kada su ƙara tashi.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ