Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 12:10 - Littafi Mai Tsarki

10 Makiyaya da yawa sun lalatar da gonar inabina. Sun tattake nawa rabo, Sun mai da nawa kyakkyawan rabo kufai da hamada.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 12:10
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Taku ta ƙare! Makiyayan da suka lalatar, suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.


Abokan gabanmu sun kusa su kori mutanenka gaba ɗaya sun kuma tattake Haikalinka.


Makiyaya da garkunansu za su zo wurinki, Za su kafa alfarwansu kewaye da ke, Kowa zai yi kiwo a makiyayarki.


“Isra'ila, na yi niyya in karɓe ku kamar ɗana, In gādar muku da kyakkyawar ƙasa Mafi kyau a dukan duniya. Na zaci za ku ce ni ne mahaifinku, Ba za ku ƙara rabuwa da bina ba.


amma kada ka auna harabar Haikalin, ka ƙyale ta, domin an ba da ita ga al'ummai, za su tattake tsattsarkan birnin nan har wata arba'in da biyu.


Saboda haka, sai ku ƙudura a ranku, a kan ba za ku damu da yadda za ku mai da jawabi ba.


Sa'an nan da aka ci Urushalima, sai dukan sarakunan Sarkin Babila suka shiga, suka zauna a Ƙofar Tsakiya. Sarakuna, su ne Nergal-sharezer, da Samgar-nebo, da Sarsekim, wato Rabsaris, da Nergal-sharezer, wato Rabmag, da dukan sauran shugabannin Sarkin Babila.


zan aiko kabilai daga arewa da bawana Nebukadnezzar, Sarkin Babila. Zan kawo su, su yi yaƙi da ƙasan nan da mazaunanta, da dukan al'umman da take kewaya da ita. Zan hallaka su sarai, in sa su zama abin ƙyama, da abin raini, da abin zargi har abada.


Zan musunci masu mulkin tsattsarkan masujadai, Saboda haka zan jawo wa Isra'ila hallaka, Zan bari a la'anta mutanena su sha zagi!”


Zan yi kuka in yi kururuwa saboda tsaunuka, Zan yi kuka saboda wuraren kiwo, Domin sun bushe sun zama marasa amfani. Ba wanda yake bi ta cikinsu. Ba a kuma jin kukan shanu, Tsuntsaye da namomin jeji, sun gudu sun tafi.


“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra'ila, ka ce musu, ‘Ku masu kiwon mutanen Isra'ila, ni Ubangiji Allah na ce, kaito, kaito, ku masu kiwon mutanen Isra'ila, kuna kiwon kanku kawai! Ashe, ba makiyaya ne suke kiwon tumaki ba?


Sai na ji wani mai tsarki yana magana, wani kuma mai tsarki ya tambayi wancan mai tsarki da ya yi magana, ya ce, “Sai yaushe za a tsai da abubuwan da suke a wahayin nan, wato hana yin hadayar ƙonawa ta yau da kullum, da zunubin da yake lalatarwa, da ba da wuri mai tsarki ga rundunar mutane don a tattake?”


Na sa guguwa ta warwatsa su a cikin al'ummai da ba su san su ba. Ƙasar da suka bari ta zama kango, ba mai kai da kawowa a cikinta. Ƙasa mai kyau ta zama kango.”


Ubangiji ya kawo dattawa da shugabannin jama'arsa a gaban shari'a. Ga laifin da ya same su da shi, “Kun washe gonakin inabi, kun cika gidajenku da abin da kuka ƙwato daga matalauta.


Garkunan da suke zaune lafiya kuwa, an yi kaca-kaca da su Saboda zafin fushin Ubangiji.


Ya rabu da wurin ɓuyarsa kamar zaki, Gama ƙasarsu ta zama marar amfani, Saboda takobin Ubangiji, da kuma zafin fushinsa.”


Sai suka warwatsu saboda rashin makiyayin kirki, suka zama abincin namomin jeji.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ