Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 10:19 - Littafi Mai Tsarki

19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini. Raunina mai tsanani ne, Amma na ce, lalle wannan azaba ce, Tilas in daure da ita.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 10:19
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zan ɗauka fushin Ubangiji ne, Gama na yi masa zunubi, Sai lokacin da ya ji da'awata, Har ya yanke mini shari'a. Zai kawo ni zuwa wurin haske, Zan kuwa ga cetonsa.


“Irmiya, ka faɗa wa mutanen baƙin ciki da ya same ka, Ka ce, ‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana, Kada su daina, saboda an buge budurwa, 'yar jama'ata, An yi mata babban rauni da dūka mai tsanani.


Na ji kuka kamar na mace wadda take naƙuda, Na ji nishi kamar na mace a lokacin haihuwarta ta fari, Na ji kukan 'yar Sihiyona tana kyakyari, Tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina, gama ina suma a gaban masu kisankai!”


Zan yi shiru, ba zan ce kome ba, Saboda ka sa na sha wahala haka.


Hawaye suna gangarawa daga idanuna kamar ruwan koguna, Saboda an hallaka mutanena.


Da dare tana kuka mai zafi, Hawaye suna zuba sharaf-sharaf a kumatunta. Dukan masoyanta ba wanda yake ta'azantar da ita. Dukan abokanta sun ci amanarta, sun zama maƙiyanta.


Ya Ubangiji, begen Isra'ila, Duk waɗanda suka rabu da kai, za su sha kunya. Waɗanda suka ba ka baya a duniya za a rubuta su Domin sun rabu da Ubangiji, maɓuɓɓugar ruwan rai.


Da ma kaina ruwa ne kundum, Idanuna kuma maɓuɓɓuga ne, Da sai in yi ta kuka dare da rana, Saboda an kashe jama'ata!


Raunin da aka yi wa jama'ata, Ya yi wa zuciyata rauni. Ina makoki, tsoro kuma ya kama ni ƙwarai.


Azaba! Ba zan iya daurewa da azaba ba! Zuciyata! Gabana yana faɗuwa da ƙarfi, Ba zan iya yin shiru ba, Gama na ji amon ƙaho da hargowar yaƙi.


Ubangiji ya ɓoye kansa daga jama'arsa, amma ni na dogara gare shi, na kafa zuciyata a gare shi.


Sa'an nan sai na ce, “Abin da ya fi mini zafi duka, Shi ne ikon Maɗaukaki ya ragu.”


Irmiya ya ce, “Ko da yake zunubanmu su ne shaidunmu, Ya Ubangiji, ka yi taimako saboda sunanka! Gama kāsawarmu ta yi yawa, Domin mun yi maka zunubi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ