Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Hosiya 9:16 - Littafi Mai Tsarki

16 An ka da mutanen Ifraimu, saiwarsu ta bushe. Ba za su yi 'ya'ya ba. Ko ma sun haihu, zan kashe 'ya'yan nan nasu waɗanda suke ƙauna.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi ’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Hosiya 9:16
10 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

in faɗa wa mutanen Isra'ila, cewa Ubangiji Allah ya ce, ‘Zan ƙazantar da Haikalina, abin fariyarku, da abin da idanunku suke jin daɗin ganinsa, da abin faranta zuciyarku. 'Ya'yanku maza waɗanda kuka bari a baya, za a kashe su da takobi.


Don haka, kamar yadda tattaka da busasshiyar ciyawa sukan yanƙwane su ƙone a wuta, saiwoyinku za su ruɓe, furanninku kuma za su bushe. Iska za ta kwashe su, domin kun ƙi abin da Ubangiji Mai Runduna, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ya koya muku.


“Duba rana tana zuwa, sa'ad da dukan masu girmankai, da mugaye za su ƙone kamar tattaka, a ran nan za su ƙone ƙurmus ba abin da zai ragu, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.


Gama sun shuka iska Don haka zu su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da zangarniya, Ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci,


An danne Ifraimu, shari'a ta murƙushe ta, Domin ta ƙudura ta bi banza.


Suna kama da ƙaramin dashe Wanda bai daɗe ba, Bai yi ko saiwar kirki ba. Sa'ad da Ubangiji ya aiko da iska, Sai su bushe, iskar ta hure su kamar ƙaiƙayi.


Saiwoyinsa da rassansa suka yi yaushi suka bushe.


zangarku bakwai kuma busassu sirara waɗanda iskar gabas ta ƙeƙasar, suka fito a bayansu.


Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, A cikin ɗakuna kuma tsoro, Zai hallaka saurayi da budurwa, Da mai shan mama da mai furfura.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ