Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Hosiya 9:11 - Littafi Mai Tsarki

11 Darajar Ifraimu za ta tashi kamar tsuntsu, Ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Hosiya 9:11
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Mazaunan Samariya suna rawar jiki Domin ɗan maraƙin Bet-awen, Mutane za su yi makoki dominsa, Firistoci matsafa, za su yi kururuwa dominsa, Da kuma darajarsa wadda ta rabu da shi.


Ya Ubangiji, me zan ce ka ba su? Me za ka ba su? Ka ba su cikin da ba ya haihuwa da busassun mama.


“Yawan ƙaruwar firistoci, yawan ƙaruwar zunubi. Zan sāke darajarsu ta zama kunya.


“La'anannu ne 'ya'yanku, da amfanin gonakinku, da 'ya'yan shanunku, da 'ya'yan tumakinku da na awakinku.


don lokaci na zuwa da za su ce, ‘Albarka tā tabbata ga matan da suke bakararru, waɗanda ba su taɓa haihuwa ba, waɗanda kuma ba a taɓa shan mamansu ba.’


Ubangiji ya ce, “Mutanen Ammon sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don haɗamarsu ta ƙasa, Suka tsaga mata masu ciki a Gileyad.


Mai yiwuwa ne mutum ya haifi 'ya'ya ɗari ya kuma yi tsawon rai, amma kome tsawon ransa ba wani abu ba ne idan ba shi da farin ciki, bai kuma sami kyakkyawar binnewa ba. Sai na ce, gara jaririn da aka haifa matacce da shi.


Bari su zama kamar katantanwu waɗanda sukan narke su yi yauƙi, Allah ya sa su zama kamar jinjirin da aka haifa matacce. Wanda bai taɓa ganin hasken rana ba.


“Za a kashe hasken mugun mutum, Harshen wutarsa ba zai ƙara ci ba.


Darajarsa kamar ta ɗan farin bijimi take, Ƙahoninsa kamar na ɓauna suke, Da su yake tunkwiyin mutane, Zai tura su zuwa ƙurewar duniya, Haka fa rundunan Ifraimu za su zama, Haka kuma dubban Manassa za su zama.”


A ɓoye za ta ci mahaifar da take biyo bayan ta haihu, da 'ya'yan da za ta haifa, saboda ba ta da wani abinci lokacin da magabtanku za su kewaye garuruwanku da yaƙi mai tsanani.


“Yusufu jakin jeji ne, Jakin jeji a gefen maɓuɓɓuga Aholakan jeji a gefen tuddai.


Na biyun kuma ya raɗa masa suna, Ifraimu, yana cewa, “Gama Allah ya wadata ni a cikin ƙasar wulakancina.”


Ba za a kāre Isra'ila ba, Dimashƙu kuma za ta rasa 'yancinta. Suriyawan da suka ragu za su sha wulakanci kamar mutanen Isra'ila. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗa.”


Ifraimu za ta zama kango a ranar hukunci. A kabilan Isra'ila na sanar da abin da zai faru, ba makawa.


Mikal, 'yar Saul fa, ba ta haihu ba har ta rasu.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ