Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Hosiya 2:19 - Littafi Mai Tsarki

19 Zan ɗaura auren da yake cikin adalci, Da bisa kan ka'ida, da ƙauna.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

19 Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Hosiya 2:19
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ina kishi a kanku saboda Allah. Gama na bashe ku ga Almasihu, domin in miƙa ku kamar amarya tsattsarka ga makaɗaicin mijinta.


Sai na ga tsattsarkan birni kuma, Sabuwar Urushalima, tana saukowa daga Sama daga wurin Allah, shiryayyiya kamar amaryar da ta yi ado saboda mijinta.


Adalci da gaskiya za su ƙarfafa ki. Za ki tsira daga shan zalunci da razana. Gama ba za su kusace ki ba.


Ƙauna da aminci za su sadu wuri ɗaya, Adalci da salama za su gamu.


Haka kuma 'yan'uwana, kun zama matattu ga Shari'a, ta wurin jikin Almasihu, domin ku zama mallakar wani, wato, wanda aka tashe shi daga matattu, domin mu ba da amfani ga Allah.


Mai amarya shi ne ango. Abokin ango kuwa da yake tsaye, yake kuma sauraron magana tasa, yakan yi farin ciki ƙwarai da jin muryar angon. Saboda haka farin cikin nan nawa ya cika.


Ba kuma zan ƙara kawar da fuskata daga gare su ba, sa'ad da na saukar da Ruhuna a kan jama'ar Isra'ila, ni Ubangiji na faɗa.”


Gama Ubangiji mai adalci ne, zai ceci Urushalima da dukan wanda ya tuba a can.


Za a zauna a Yahuza da Urushalima dukan tsararraki har abada.


Mahaliccinki zai zama kamar miji a gare ki, Sunansa Ubangiji Mai Runduna! Allah Mai Tsarki na Isra'ila mai fansarki ne, Shi ne mai mulkin dukan duniya!


Idan kun yi rantsuwa kuka ce, ‘Har da ran Ubangiji kuwa,’ Da gaskiya, da aminci, da adalci, Sa'an nan sauran al'umma za su so in sa musu albarka, Za su kuma yabe ni.”


Kina kama da amarya Wadda mijinta ya rabu da ita, tana baƙin ciki ƙwarai. Amma Ubangiji yana kiranki zuwa gare shi, ya ce,


“Sa'ad da na sāke wucewa kusa da ke, na dube ki, ga shi, kin kai lokacin da za a ƙaunace ki, sai na yafe miki tufata, na rufe tsiraincinki, na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, ni Ubangiji Allah na faɗa.


Ubangiji ya ce, “Zan warkar musu da riddarsu. Zan kuma ƙaunace su sosai, Gama fushina zai huce.


A wannan rana fa, ni Ubangiji Mai Runduna, zan shafe sunayen gumaka daga ƙasar, har da ba za a ƙara tunawa da su ba. Zan kuma kawar da annabawa da mugayen aljannu.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ