Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Hosiya 2:15 - Littafi Mai Tsarki

15 Can zan ba ta gonar inabi, In mai da kwarin Akor, wato wahala, ƙofar bege. A can za ta amsa mini kamar a kwanakin ƙuruciyarta, Kamar lokacin da ta fito daga ƙasar Masar.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

15 A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Hosiya 2:15
33 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Za su zauna lafiya a cikinta, za su gina gidaje, su yi gonakin inabi. Za su zauna gonakin inabi. Za su zauna lafiya sa'ad da na hukunta maƙwabtansu waɗanda suka wulakanta su. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allahnsu.’ ”


in tafi in yi shelar abin da Ubangiji ya ce a kunnen Urushalima, in ce, “Na tuna da amincinki a lokacin ƙuruciyarki, Da ƙaunarki kamar ta amarya da ango. Yadda kika bi ni a cikin jeji, da a ƙasar da ba a shuka ba.


“A lokacin da Isra'ila yake yaro, na ƙaunace shi, Daga cikin Masar na kirawo ɗana.


Suka tara tsibin duwatsu a kansu. Tsibin duwatsun kuwa yana nan har wa yau. Sa'an nan Ubangiji ya huce daga zafin fushinsa. Domin haka ana kiran wurin Kwarin Akor, wato azaba, har wa yau.


Da suka iso, suka tara jama'ar Ikkilisiya suka ba da labarin dukan abin da Allah ya aikata ta wurinsu, da kuma yadda ya buɗe wa al'ummai ƙofar bangaskiya.


Ni ne ƙofar. Kowa ya shiga ta wurina zai sami ceto, ya kai ya kawo, ya kuma yi kiwo.


Zan komo da mutanena ƙasarsu, Za su giggina biranensu da suka rurrushe, Su zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi, su sha ruwan inabin. Za su yi lambuna, su ci amfaninsu.


Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin kuruciyarki. Zan ƙulla madawwamin alkawari da ke.


A cikin aikata dukan abubuwanki na banƙyama kuma, da karuwancinki, ba ki tuna da kwanakin kuruciyarki ba, lokacin da kike tsirara tik, kina birgima cikin jinin haihuwarki.


“Sa'ad da na sāke wucewa kusa da ke, na dube ki, ga shi, kin kai lokacin da za a ƙaunace ki, sai na yafe miki tufata, na rufe tsiraincinki, na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, ni Ubangiji Allah na faɗa.


Mutane za su gina gidaje su kuwa zauna a cikinsu, ba waɗansu dabam za su mori gidajen ba. Za su dasa gonakin inabi su kuwa ji daɗin ruwan inabi, ba waɗansu dabam za su sha shi ba. Mutanena za su yi tsawon rai kamar itatuwa. Za su ci cikakkiyar moriyar abubuwan da suka yi aikinsu.


Ku koma mafakarku, ku ɗaurarru masu sa zuciya. Gama yanzu zan sāka muku har ninki biyu.


Da na tuna da wannan, sai na sa zuciya ga gaba.


Gama haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗa, ‘Gidaje, da gonaki, da gonakin inabi, za a sāke sayensu a ƙasan nan.’ ”


Sa'an nan jama'arsa suka gaskata alkawarinsa, Suka raira yabo gare shi.


Sai Isra'ilawa suka raira waƙa, suka ce, “Rijiya, ki ɓuɓɓugo da ruwa Mu kuwa za mu raira waƙa mu gaishe ta!


Ni ne Ubangiji Allahnku tun daga ƙasar Masar, Zan kuma sa ku zauna cikin alfarwai, Kamar lokatan ƙayyadaddun idodi.


Za su yi mini sujada, za su kai tumakinsu da shanunsu wurin kiwo a kwarin Sharon a wajen yamma, da kuma a kwarin Akor a wajen gabas.


Zan ɓata inabinta da itatuwan ɓaure Waɗanda take cewa, ‘Waɗannan su ne hakkina Wanda samarina suka ba ni.’ Zan sa su zama kurmi, Namomin jeji su cinye su.


Isra'ila, sai ka faɗi irin muguntar Da maƙiyanka suka tsananta maka da ita, Tun kana ƙarami!


“Yanzu kin ce, ‘Kai ne mahaifina, Ka ƙaunace ni tun ina cikin ƙuruciyata.


Gama na san irin shirin da na yi muku, ni Ubangiji na faɗa. Shirin alheri, ba na mugunta ba. Zan ba ku gabata da sa zuciya.


“Ubangiji Allah ya ce, ‘Sa'ad da na tattara mutanen Isra'ila daga cikin sauran al'umma, inda na watsar da su, na kuma bayyana tsarkina a cikinsu a kan idon al'ummai, sa'an nan za su zauna a ƙarsarsu wadda na ba bawana Yakubu.


Ta wurin annabi Ubangiji ya fito da mutanen Isra'ila daga Masar, Ta wurin annabi kuma ya kiyaye su.


Ubangiji ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku Tun daga ƙasar Masar. Banda ni ba ku san wani Allah ba, Banda ni kuma ba wani mai ceto.


Suka daina bauta wa Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga magabtan da suke kewaye da su.


Da yake abu ne mai sauƙi a gare shi ya bi hanyar zunuban Yerobowam ɗan Nebat, sai ya auro Yezebel 'yar Etba'al, Sarkin Sidon, ya kuma bauta wa gunkin nan Ba'al, ya yi masa sujada.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ