Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Hosiya 12:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Mutanen Ifraimu sun ce, ‘Hakika, mun zama attajirai, Mun samar wa kanmu dukiya. A cikin harkokinmu ba za a sami wata mugunta ba.’

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Hosiya 12:8
29 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Tun da ka ce, kai mai arziki ne, cewa ka wadata ba ka bukatar kome, ba ka sani ba kuwa kai ne matsiyacin, abin yi wa kaito, matalauci, makaho, tsirara kuma.


Kada ku dogara da aikin kama-karya. Kada ku sa zuciya za ku ci ribar kome ta wurin fashi. In kuwa dukiyarku ta ƙaru, Kada ku dogara gare ta.


da kuma yawan tankiya a cikin mutane masu ɓataccen hankali, waɗanda har gaskiya ta ƙaurace musu, suna tsammani bin Allah hanya ce ta samu.


Masu sayensu za su yanyanka su, ba za a kuwa hukunta su ba. Masu sayar da su kuma za su yi hamdala gare ni, su ce sun sami dukiya. Makiyayansu kuwa ba su ji tausayinsu ba.


Ga yadda al'amarin mazinaciya yake, takan yi sha'aninta sa'an nan ta yi wanka ta ce, “Ban yi laifin kome ba!”


Akwai waɗansu mutanen da suke ganin kansu tsarkaka ne, alhali kuwa ƙazamai ne su.


“Duba, ga mutumin da bai dogara ga Allah Don ya sami zaman lafiyarsa ba. A maimakon haka, sai ya dogara ga wadatarsa. Yana neman zaman lafiyarsa ta wurin muguntarsa.”


Mutanen da suke dogara ga dukiyarsu, Waɗanda suke fariya saboda yawan wadatarsu?


Kada ku ce a zuciya, ‘Ai, ikona da ƙarfin hannuwana ne suka kawo mini wannan wadata.’


Masu dukiyar duniyar nan kuwa ka gargaɗe su kada su nuna alfarma, kada kuwa su dogara da dukiya marar tabbata, sai dai ga Allah, wanda yake ba mu kome a yalwace don mu ji daɗinsa.


Sai ya ce musu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane. Amma Allah ya san zukatanku. Abin da mutane suke girmamawa ƙwarai, ai, abin ƙyama ne a gun Allah.


Ba baran da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗaya, ko kuwa ya amince wa ɗayan, ya raina ɗayan. Ba dama ku bauta wa Allah da dukiya gaba ɗaya.”


Zan kuma ce wa raina, “Lalle ina da kaya masu yawa a jibge, tanadin shekara da shekaru. Bari in huta, in yi ta ci, in yi ta sha, ina shagali.” ’


Shi kuwa mutumin, don yana son baratar da kansa, ya ce wa Yesu, “To, wane ne ɗan'uwa nawa?”


“Kun faɗi mugun abu a kaina,” in ji Ubangiji, “Amma kun ce, ‘Me muka ce a kanka?’


Domin haka sukan miƙa hadaya ga tarunsa, Su ƙona turare ga ragarsu, Domin su ne suka jawo musu wadata, da abinci mai yawa.


Ƙaƙa za ka ce ba ka ƙazantar da kanka ba, Ba ka taɓa bin gunkin nan Ba'al ba? Ka duba hanyarka ta zuwa cikin kwari, ka san abin da ka yi. Kana kama da taguwa, mai yawon neman barbara.


‘Ba mu da laifi, hakika kuwa, Ubangiji bai yi fushi da mu ba.’ Amma ni Ubangiji zan hukunta ku, Domin kun ce ba ku yi zunubi ba.


Kun gajiyar da Ubangiji Mai Runduna da maganganunku, amma kun ce, “Ƙaƙa muka gajiyar da shi?” Kuna cewa, “Ubangiji yana ganinsu, dukan masu aikata mugunta mutanen kirki ne, yana kuwa ƙaunarsu.” Kuna kuma cewa, “Ina Allah yake wanda yake shi adali ne?”


Saboda yawan hikimarka na yin kasuwanci, ka ƙara dukiyarka, Sai dukiyarka ta sa zuciyarka ta cika da alfarma.’


Suna ciyar da kansu da zunubin mutanena, Suna haɗamar ribar muguntarsu.


Sa'ad da suka sami wurin kiwo, suka ƙoshi, Sai suka yi girmankai, Suka manta da ni.


Ya mutanen Isra'ila, ku komo wurin Ubangiji Allahnku, Gama zunubinku ya sa kun yi tuntuɓe.


Ubangiji yana ƙin masu yin awo da ma'aunin zamba, amma yana farin ciki da masu yin awo da ma'auni na gaskiya.


Kamar kwando cike da tsuntsaye, Haka nan gidajensu suke cike da cin amana, Don haka suka zama manya, suka sami dukiya.


Kuna ce wa kanku, “Mun ƙosa keɓaɓɓun kwanakin nan su wuce, Mu sami damar yin kasuwancinmu. Yaushe Asabar ɗin za ta ƙare ne? Ko mā sami damar kai hatsinmu kasuwa, Mu sayar musu da tsada, Mu yi awo da ma'aunin zalunci, Mu daidaita ma'auni yadda za mu cuci mai saya?


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ