Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Hosiya 12:7 - Littafi Mai Tsarki

7 Ubangiji ya ce, “Ɗan kasuwa wanda yake da ma'aunin algus a hannunsa. Yana jin daɗin yin zalunci.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Hosiya 12:7
28 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji yana ƙin masu yin awo da ma'aunin zamba, amma yana farin ciki da masu yin awo da ma'auni na gaskiya.


Ga shi kuwa, zaluncin da kuka yi na hakkin masu girbi a gonakinku yana ta ƙara, kukan masu girbin kuwa ya kai ga kunnen Ubangijin Runduna.


Ya ce da dillalan tattabarai, “Ku kwashe waɗannan daga nan, kada ku mai da Haikalin Ubana kasuwa.”


Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan zo wurinku domin in yi shari'a. Nan da nan zan tabbatar da laifin masu yin sihiri, da na mazinata, da na masu shaidar zur, da na masu zaluntar ma'aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu, da baƙi, da waɗanda ba su ganin girmana.”


Kowace tukunya da take a Urushalima da Yahuza za ta zama tsattsarka ga Ubangiji Mai Runduna domin dukan masu miƙa hadaya su ɗauka su dafa naman hadaya a cikinsu. A wannan rana ba za a ƙara samun mai ciniki a Haikalin Ubangiji Mai Runduna ba.


Mutanen kirki sun ƙare a duniya, Ba nagarta a cikin mutane. Dukansu suna kwanto don su zub da jini. Kowa yana farautar ɗan'uwansa da tarko.


Kun matsa wa talakawa lamba, Kun ƙwace musu abincinsu. Saboda haka kyawawan gidajen nan da kun gina da dutse, Ba za ku zauna a cikinsu ba, Ba kuwa za ku sha ruwan inabin nan Daga kyawawan gonakin inabinku ba.


Ku kasa kunne ga wannan, ya ku matan Samariya, Ku da kuka yi ƙiba kamar turkakkun shanu, Ku da kuke wulakanta kasassu, Kuna yi wa matalauta danniya, Kukan umarci mazajenku, Ku ce, “Kawo mini abin sha!”


Ka yi shela ga mazaunan fādar Ashdod da Masar, ka ce, “Duk ku taru a Samariya ku ga irin babban shashancin da ake yi a can, ku ga irin laifofin da ake aikatawa a birnin.”


Sun tattake marasa ƙarfi da kāsassu, Suna tunkuɗe matalauta su wuce. Tsofaffi da samari sukan tafi wurin karuwan Haikali. Ta haka suke ɓata sunana mai tsarki.


Mutanen ƙasar sun yi zalunci, sun yi fashi, sun zalunci matalauta da masu fatara. Ba su yi wa baƙo adalci ba, sai cuta.


Ka faɗa wa Urushalima abin da ni Ubangiji Allah na ce mata.” Ubangiji ya ce, “Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan'ana ne. Mahaifinki Ba'amore ne, mahaifiyarki kuwa Bahittiya ce.


Za a yi ta cutar juna. Matasa ba za su girmama manyansu ba, talakawa ba za su girmama na gaba da su ba.


Ubangiji yana son ma'aunai su zama na gaskiya, kowane abin sayarwa kuma ya zama daidai.


To, ga ni nan, ku shaida a kaina a gaban Ubangiji da gaban wanda Ubangiji ya naɗa sarki. Takarkari ko jakin wa na ƙwace? Wa kuma na zalunta, ko na wulakanta? A wurin wa na karɓi hanci don in danne gaskiya? Sai ku shaida, ni kuwa zan mayar masa.”


Taku ta ƙare, ku masu shirya mugunta, Masu tsara mugunta a gadajensu! Sa'ad da gari ya waye, sai su aikata ta, Domin ikon aikatawa yana hannunsu.


Saboda yawan hikimarka na yin kasuwanci, ka ƙara dukiyarka, Sai dukiyarka ta sa zuciyarka ta cika da alfarma.’


Sai ya ce, “Wannan mugunta ce.” Sa'an nan ya tura ta cikin kwandon, ya rufe bakin kwandon da murfi na darma mai nauyi.


Ga jawabin da Ubangiji ya yi, “Ku kiyaye gaskiya ku yi adalci, gama cetona yana zuwa nan da nan, za a kuwa bayyana adalcina.


Ku komo wurin Ubangiji, ku roƙe shi, Ku ce, “Ka gafarta mana zunubanmu, Ka karɓe mu saboda alherinka, Mu kuwa za mu yabe ka da bakinmu.


“Koyanzu,” in ji Ubangiji, “Ku juyo wurina da zuciya ɗaya, Da azumi, da kuka, da makoki,


“Ni Ubangiji Mai Runduna, na ce ku yi shari'ar gaskiya, bari kowa ya nuna alheri da jinƙai ga ɗan'uwansa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ