Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Hosiya 10:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Za a hallaka masujadan tuddai na Awen inda Isra'ila suke yin zunubi, Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma a bagadansu. Za su ce wa manyan duwatsu, “Ku rufe mu!” Su ce wa tuddai, “Ku faɗo bisa kanmu!”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Hosiya 10:8
32 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sa'an nan ne za su fara ce wa manyan duwatsu, ‘Ku faɗo a kanmu,’ su kuma ce da tsaunuka, ‘Ku binne mu.’


suna ce wa duwatsun, “Ku faɗo a kanmu, ku ɓoye mu daga idon wanda yake a zaune a kan kursiyin, da kuma fushin Ɗan Ragon nan,


Mutane za su ɓuya a kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa, sa'ad da ya zo domin ya girgiza duniya.


Ga shi kuma, suna tafiya zuwa halaka, Masar za ta tattara su, Memfis za ta binne su. Ƙayayuwa za su mallaki abubuwan tamaninsu na azurfa. Sarƙaƙƙiya za ta tsiro a cikin alfarwansu.


Waɗanda suka yi rantsuwa da gumakan Samariya, Waɗanda suka ce, ‘Na rantse da gunkin Dan, Da ran gunkin Biyer-sheba,’ Irin waɗannan mutane za su fāɗi, Ba za su ƙara tashi ba.”


ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya ne suke girma a ƙasar jama'ata. Ku yi kuka domin dukan gidajen da mutane suke murna a cikinsu dā, domin kuma birnin da yake cike da jin daɗi a dā.


A waɗannan kwanaki kuwa mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su same ta ba, za su ƙagauta su mutu, mutuwa kuwa sai ta guje musu.


Ku mutanen Lakish, ku ɗaura wa dawakai karusai, Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, Gama an iske laifofin Isra'ila cikinku.


Duk wannan kuwa saboda laifin Yakubu ne, Da laifin Isra'ila. Mene ne laifin Yakubu? Ashe, ba bautar gumaka da zaluncin da ake yi a Samariya ba? Mene ne kuma laifin Yahuza? Ashe, ba bautar gumaka da zaluncin da ake yi a Urushalima ba?


Mazaunan Samariya suna rawar jiki Domin ɗan maraƙin Bet-awen, Mutane za su yi makoki dominsa, Firistoci matsafa, za su yi kururuwa dominsa, Da kuma darajarsa wadda ta rabu da shi.


Zuciyarsu ta munafunci ce, Yanzu tilas za su ɗauki hakkin laifinsu, Ubangiji zai farfashe bagadansu da ginshiƙansu.


“Ku busa ƙaho cikin Gibeya, Ku busa kakaki cikin Rama, Ku yi gangami cikin Bet-awen, Ku yi rawar yaƙi, ya ku Biliyaminu!


“Ko da yake mutanen Isra'ila suna karuwanci, Kada kuma mutanen Yahuza su yi laifi. Kada ku tafi Gilgal, Ko ku haura zuwa Bet-awen. Kada ku yi rantsuwa da cewa, ‘Har da zatin Ubangiji!’


Suna miƙa sadaka a bisa ƙwanƙolin duwatsu. Suna yin hadaya a bisa tuddai, Da kuma a gindin itacen oak, da aduruku, da katambiri, Domin suna da inuwa mai kyau. Don haka 'ya'yanku mata suke karuwanci, Surukanku mata suke yin zina.


Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su tsiro su yi girma a cikin dukan fādodi da garuruwa masu garuka, diloli da mujiyoyi za su zauna a cikinsu.


Sa'ad da aka gama duka, sai dukan Isra'ilawa da suka hallara, suka bi cikin biranen Yahuza, suka farfashe al'amudan, suka ragargaza Ashtarot, suka farfashe masujadai da bagadai duka da suke a Yahuza da Biliyaminu, da na Ifraimu da Manassa har suka hallakar da su duka. Sa'an nan dukan jama'ar Isra'ila suka koma garuruwansu, ko wanne zuwa mahallinsa.


Yosiya ya kuma rushe bagaden da yake a Betel, wanda Yerobowam ɗan Nebat ya gina, wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi, tare da tudun, ya farfashe duwatsun, ya niƙe su, sun zama gari, ya kuma ƙone Ashtoret.


Ubangiji zai rabu da Isra'ila saboda zunuban Yerobowam waɗanda ya yi, da kuma waɗanda ya sa mutanen Isra'ila su yi.”


Wannan zunubi ya zama sanadi ga gidan Yerobowam, har ya isa a shafe gidan, a hallaka shi ƙaƙaf.


Bisa ga umarnin Ubangiji, sai annabin ya ta da murya, ya ce, “Ya bagade, bagade, Ubangiji ya ce za a haifi ɗa a gidan Dawuda, sunansa Yosiya wanda zai miƙa firistoci na masujadan tuddai hadaya a kanka, wato firistoci waɗanda suke ƙona turare. Za a ƙone ƙasusuwan mutane a bisa kanka.”


Sa'an nan na ɗauki abin zunubin nan, wato siffar maraƙin da kuka yi, na ƙone, na farfashe, na niƙe shi lilis, ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da garin a rafi wanda yake gangarowa daga dutsen.


Da suka ji motsin Allah yana yawo a gonar da sanyin la'asariya, sai mutumin da matarsa suka ɓuya wa Ubangiji Allah cikin itatuwan gonar.


“Don haka zan shinge hanyarta da ƙaya, Zan gina mata garu don kada ta sami hanyar fita.


Ubangiji ya ce, “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra'ila! Tun daga wancan lokaci kuka yi ta ci gaba. Ashe, yaƙi ba zai tarshe su a Gibeya ba?


Zan hallakar da wuraren sujada na zuriyar Ishaku. Za a hallakar da tsarkakan wurare na Isra'ila. Zan fāɗa wa zuriyar sarki Yerobowam da yaƙi.”


Ke Nineba kuma za ki bugu, Za a ɓoye ki. Za ki nemi mafaka a wurin maƙiyinki.


Sa'ad da Ubangiji ya zo domin ya girgiza duniya, jama'a za su ɓuya a cikin kogwannin tuddai da ramummukan duwatsu, suna ƙoƙari su ɓuya daga fushinsa, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa.


Ya mutanen Samariya, ina ƙin maraƙinku na siffa. Ina jin haushinsu ƙwarai! Sai yaushe za su rabu da gumaka?


Zan ragargaje ƙyamaren ƙofofin birnin Dimashƙu, In kawar da masu sarautar Bet-eden da na kwarin Awen. Za a kwashe mutanen Suriya ganima zuwa ƙasar Kir.”


“Ran da na hukunta mutanen Isra'ila saboda zunubansu, Zan hallakar da bagadan Betel. Za a kakkarya zankayen bagaden, Su fāɗi ƙasa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ