Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Habakkuk 1:15 - Littafi Mai Tsarki

15 Kaldiyawa sukan kama mutane da ƙugiya, Sukan jawo su waje da tarunsa, Sa'an nan su tara su cikin ragarsu, Su yi murna da farin ciki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

15 Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Habakkuk 1:15
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Da yake Ubangiji Mai Tsarki ne Ya riga ya yi alkawari, Ya ce, “Hakika kwanaki za su zo Da za a jawo ku da ƙugiyoyi, Kowannenku zai zama kamar kifi a ƙugiya.


“Ga shi, ina aiko da masunta da yawa,” in ji Ubangiji, “za su kuwa kama su, daga baya kuma zan aika da mafarauta da yawa, za su farauce su daga kowane tsauni, da tudu, da kogwannin duwatsu.


Yakan jira a inda ya ɓuya kamar zaki. Yakan kwanta yana fakon wanda zai kama, Har ya kama shi da tarkonsa ya tafi da shi!


Mazaunan duniya kuma, sai su yi ta alwashi a kansu, suna ta shagali, suna a'aika wa juna da kyauta, domin annabawan nan biyu dā sun azabtar da mazaunan duniya.


Duk da haka, don kada mu ba su haushi, ka je teku ka yi fatsa, kifin da ka fara kamawa kuwa shi za ka ɗauka. In ka buɗe bakinsa za ka sami shekel guda a ciki. To, sai ka ɗauki shekel ɗin nan ka kai musu, wato, nawa da naka.”


Kamar yadda ya yi farin ciki saboda gādon jama'ar Isra'ila, da ya zama kufai marar amfani, haka nan zan yi da shi, wato Seyir. Zai zama kufai marar amfani, wato Dutsen Seyir da dukan Edom. Sa'an nan mutane za su sani ni ne Ubangiji!”


“Ɗan mutum, da yake Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Madalla, Urushalima ta rushe, ƙofa ta buɗu, yanzu zan wadata da yake ta zama kufai,’


Gama Ubangiji Allah ya ce, “Da yake kun tafa hannuwanku, kun buga ƙafafunku, kuka yi murna don nuna dukan ƙiyayyarku da ƙasar Isra'ila,


“Saboda kuna murna, kuna farin ciki, Ku da kuka washe gādona, Saboda kuma kuna tsalle kamar karsana a cikin ciyawa, Kuna haniniya kamar ingarmu,


Duk wanda sana'arsa ta kama kifi ce a Kogin Nilu zai yi ƙugi ya yi kuka, gama ƙugiyoyinsa da tarunansa za su zama marasa amfani.


Wanda duk ya ji Maganar Mulki bai kuma fahimce ta ba, sai Mugun ya zo ya zăre abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya faɗa a hanya.


“Gama an sami mugaye, a cikin jama'ata, Suna kwanto kamar masu kafa ashibta. Sun ɗana tarko su kama mutane.


Gama ka mai da mutane kamar kifaye a cikin teku, Kamar abubuwa masu rarrafe da ba su da shugaba.


“Ruwan inabi kuma yana yaudarar mai fariya, Don haka ba ya zama a gida. Haɗamarsa tana da fāɗi kamar Lahira, Kamar kuma mutuwa yake, ba ya ƙoshi. Ya tattara wa kansa al'ummai duka, Ya kwaso wa kansa mutane duka.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ