Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Fitowa 9:14 - Littafi Mai Tsarki

14 A wannan karo, ni da kaina zan kawo maka, da fādawanka, da jama'arka annoba, domin ka sani babu mai kama da ni a dukan duniya.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

14 ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Fitowa 9:14
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Fir'auna ya ce, “Gobe ne.” Musa kuwa ya ce, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani allah kamar Ubangiji Allahnmu.


Ina yi wa duk mai jin maganar annabcin littafin nan kashedi, in wani ya yi wani ƙari a kanta, Allah zai ƙara masa bala'in da aka rubuta a littafin nan.


Saboda haka, bala'inta zai aukar mata rana ɗaya, Mutuwa, da baƙin ciki, da yunwa. Za a kuma ƙone ta, Domin Ubangiji Allah da yake hukunta ta Mai Ƙarfi ne.”


Domin haka zan buge ku da ciwo, In maishe ku kufai saboda zunubanka.


Zan mai da wannan birni abin ƙyama, abin raini, dukan wanda ya wuce wurin zai yi mamaki, ya yi tsaki saboda dukan masifun da suka auka wa birnin.


Ya Ubangiji, ba wani kamarka, Kai mai girma ne, Sunanka kuma yana da girma da iko.


Ku tuna da abin da ya faru tuntuni, Ku sani, ni kaɗai ne Allah, Ba kuwa wani mai kama da ni.


Ba wani allah kamarka, ya Ubangiji, Ba ko ɗaya, ba wanda zai iya aikata abin da kake aikatawa.


Ya Ubangiji, ba wani kamarka, ba kuma wani Allah sai kai, bisa ga duk abin da muka ji da kunnuwanmu.


sai ka kasa kunne ga addu'arsu. Idan ɗaya daga cikin jama'arka Isra'ila ya matsu a zuciyarsa, ya ɗaga hannuwansa sama yana addu'a wajen wannan Haikali,


Bisa ga dukan abin da muka ji, kai mai girma ne, ya Ubangiji Allah. Ba kamarka, in banda kai kuma babu wani Allah.


Mun shiga uku, wa zai cece mu daga hannun allolin nan masu iko? Waɗannan suka karkashe Masarawa a hamada!


sai ni ma in tayar muku da fushi, in hukunta ku har riɓi bakwai, saboda zunubanku.


“Idan har yanzu kuka tayar mini, ba ku kasa kunne gare ni ba, sai in ƙara yawan hukuncinku har sau bakwai, saboda zunubanku.


“Amma idan duk da haka ba ku kasa kunne gare ni ba, sai in tsananta hukuncinku har sau bakwai saboda zunubanku.


Gama da ni kaina na miƙa dantsena na buge ka da jama'arka da annoba, ai, da an hallakar da ku a duniya ƙaƙaf.


“Ya Ubangiji, wane ne kamarka a cikin alloli? Wa yake kamarka a cikin ɗaukaka da tsarki? Mai banrazana cikin mafifitan ayyuka, mai aikata mu'ujizai.


‘Ya Ubangiji Allah, kai ne ka fara nuna wa baranka ɗaukakarka da ikonka. Ba wani Allah a Sama ko a duniya da zai aikata ayyuka na banmamaki irin naka.


An nuna muku wannan don ku sani Ubangiji shi ne Allah, banda shi, ba wani kuma.


“Ni ne Ubangiji, ba wani Allah sai ni. Zan ba ka irin ƙarfin da kake bukata, Ko da yake kai ba ka san ni ba.


Wane ne ba zai ji tsoronka ba, ya Sarkin dukan al'ummai? Ka isa a ji tsoronka, Gama babu kamarka a cikin dukan masu hikima na al'ummai, Da kuma cikin dukan mulkokinsu, Ba wani kamarka.


Aka kore shi daga cikin mutane, aka ba shi hankali irin na dabba. Ya tafi ya zauna tare da jakunan jeji, yana ta cin ciyawa kamar sa. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne yake sarautar 'yan adam, yakan kuma ba da ita ga wanda ya ga dama.


Haruna ya miƙa sandansa a bisa ruwayen Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka rufe ƙasar Masar.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ