Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Firistoci 26:43 - Littafi Mai Tsarki

43 Amma za su fita daga ƙasar, ƙasar kuwa za ta ji daɗin hutunta muddin ba su ciki, tana zaman kango. Amma za su tuba saboda sun ƙi kula da ka'idodina, suka yi watsi da dokokina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

43 Gama za su gudu su bar ƙasar, ƙasar kuwa ta ji daɗin asabbatanta yayinda take kango muddin ba su ciki. Za su biya hukuncin zunubansu domin sun ƙi dokokina, suka kuma yi ƙyamar farillaina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Firistoci 26:43
28 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Don ƙwallafa rai ga al'amuran halin mutuntaka gāba ne da Allah, gama ba ya bin Shari'ar Allah, ba kuwa zai iya ba.


Idan kuma kuka yi watsi da dokokina, ba ku kuwa kula da ka'idodina ba, har kuka ƙi kiyaye umarnaina, kuka karya alkawarina,


Ba dama duniya ta ƙi ku, amma ni take ƙi, don na shaide ta a kan ayyukanta mugaye ne.


A wata guda na hallaka makiyayan nan uku, gama ban jure da su ba, su ma sun gaji da ni.


Kun ƙi wanda ya tsaya a kan adalci, Da mai faɗar ainihin gaskiya a gaban shari'a.


Domin haka Ubangiji ya shirya bala'i, ya kuma aukar mana da shi, gama Ubangiji Allahnmu mai adalci ne cikin dukan abin da ya aikata, amma mu ba mu bi maganarsa ba.


Gama na tuba saboda na rabu da kai, Bayan da aka ganar da ni, sai na sunkuyar da kai, Kunya ta kama ni, na gigice, Domin ina ɗauke da wulakancin ƙuruciyata.’


Ka hukunta jama'arka, ya Ubangiji, A cikin azaba sun yi addu'a gare ka.


Na sani ka'idodinka na adalci ne, ya Ubangiji, Ka hore ni, domin kai mai aminci ne.


Horon da aka yi mini ya yi kyau, Domin ya sa na koyi umarnanka.


Kafin ka hore ni nakan yi kuskure, Amma yanzu ina biyayya da maganarka.


Kun ƙi in tsauta muku, Kun yi watsi da umarnaina.


Ku yi kira gare ni sa'ad da wahala ta zo, Zan cece ku, Ku kuwa za ku yabe ni.”


“Mai farin ciki ne mutumin da Allah ya hora, Kada ka tsargu sa'ad da ya tsauta maka.


Amma sa'ad da yake wahala, sai ya roƙi jinƙan Ubangiji Allahnsa, ya ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.


haka kuma ni na tayar musu, na kai su ƙasar maƙiyansu. Amma idan sun ƙasƙantar da kangararriyar zuciyarsu, suka tuba, suka bar muguntarsu,


Zan lalatar da masujadanku, in rurrushe bagaden ƙona turarenku, in jefar da gawawwakinku a kan gumakanku, raina kuwa zai ji ƙyamarku.


Zan kafa wurin zamana a tsakiyarku, ba kuwa zan gaji da ku ba.


Ubangiji zai ɗauka wa jama'arsa fansa, Zai ji ƙan bayinsa, Sa'ad da ya ga ƙarfinsu ya kāsa, Ba kuma wanda ya ragu, bawa ko ɗa.


don maganar ta cika wadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Irmiya, har lokacin da ƙasar take shan hutawar asabatanta na zamanta kango har shekara saba'in, ta kiyaye asabatai.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ