Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Firistoci 26:20 - Littafi Mai Tsarki

20 Za ku ɓarnatar da ƙarfinku a banza gama ƙasarku ba za ta ba da amfaninta ba, itatuwan ƙasar kuma ba za su ba da 'ya'ya ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

20 Ƙarfinku zai ƙare a banza domin ƙasarku ba za tă ba da hatsi ba, balle itatuwan ƙasar su ba da ’ya’ya.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Firistoci 26:20
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Na ce, “Na yi aiki, amma a banza ne. Na mori ƙarfina, amma ban ƙulla kome ba.” Duk da haka na dogara ga Ubangiji, ya daidaita al'amura, Shi zai sāka mini abin da na yi.


Idan ba Ubangiji ne ya gina gidan ba, Aikin magina banza ne. Idan ba Ubangiji ne ya tsare birnin ba, Ba wani amfani a sa matsara su yi tsaro.


don kada Ubangiji ya yi fushi da ku, ya rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.


Ba Ubangiji Mai Runduna ne ya sa mutanen duniya, su yi wahala, wuta ta cinye ba? Sun kuma gajiyar da kansu a banza?


sa'an nan zan ba da ruwan sama a lokacinsa, ƙasar kuwa za ta ba da albarkarta, itatuwan gonaki kuma za su ba da 'ya'yansu.


Amma kun ba ni tsoro, kada ya zamana na yi wahala a kanku a banza!


Ni na yi shuka, Afolos ya yi banruwa, amma Allah ne ya girmar.


A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai ya iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don ya ɗebo mudu hamsin, sai ya tarar da mudu ashirin kawai.


Amma ko da za su toho su yi fure a safiyar da kuka dasa su, duk da haka ba za a girbe kome ba. Wahala ce kaɗai da azabar da ba ta warkuwa.


Ya mai da ƙasa mai dausayi ta zama mai gishiri, marar amfani, Saboda muguntar waɗanda suke zaune a can.


Ka sa ƙayayuwa su tsiro maimakon alkama, Tsire-tsire marasa amfani kuma maimakon sha'ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.


Ƙwari za su cinye dukan itatuwanku da dukan amfanin ƙasarku.


“La'anannu ne 'ya'yanku, da amfanin gonakinku, da 'ya'yan shanunku, da 'ya'yan tumakinku da na awakinku.


Gama fushina ya kama wuta, Tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za ta cinye duniya da dukan amfaninta, Za ta kama tussan duwatsu.


Isra'ila, kin manta da Allah wanda ya kuɓutar da ke, wanda ya kāre ki kamar babban dutse. Kin dasa wa kanki lambuna masu ni'ima don ki yi wa gumaka sujada.


Sun shuka alkama, sun girbe ƙayayuwa, Sun gajiyar da kansu, amma ba su amfana da kome ba. Za su sha kunya saboda abin da suke girbe, Saboda zafin fushin Ubangiji.”


In ka yi noma, ƙasar ba za ta ƙara ba ka cikakken amfaninta ba, za ka zama mai yawo barkatai, mai kai da kawowa a duniya.”


Sai Iliya ya tafi. A lokacin kuwa yunwa ta tsananta a Samariya.


Zan sa ta daina farin cikinta, Da idodinta, da kiyaye lokatan amaryar wata, Da hutawar ranar Asabar, Da ƙayyadaddun idodinta.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ