Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Filibbiyawa 1:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Domin Allah shi ne mashaidina a kan yadda nake begenku duka, da irin ƙaunar da Almasihu Yesu yake yi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Allah shi ne shaidata, ya san yadda nake ƙaunarku duka da ƙaunar Kiristi Yesu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Filibbiyawa 1:8
24 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Saboda haka ya 'yan'uwana, ƙaunatattuna, waɗanda nake bege, ku da kuke abin farin cikina da abin taƙamata kuma, ku dage ga Ubangiji, ya ku ƙaunatattuna.


Domin kuwa Allah, wanda nake bauta wa a ruhuna ta yin bisharar Ɗansa, shi ne mashaidina a kan yadda kullum ba na fasa ambatonku a cikin addu'ata,


Sa'ad da nake tunawa da hawayenka, nakan yi began ganinka dare da rana, domin in yi farin ciki matuƙa.


Saboda kuma muna Kaunarku ƙwarai da gaske ne shi ya sa muke jin daɗin ba da har rayukanmu ma saboda ku, ba yi muku bisharar Allah kaɗai ba, don kun shiga ranmu da gaske.


Gaskiya nake faɗa, ni na Almasihu ne, ba ƙarya nake yi ba. Lamirina, ta wurin Ruhu Mai Tsarki, yana ba da shaida,


Ga shi nan, na komo maka da shi kamar gudan zuciyata.


Ashe, Ifraimu ba ƙaunataccen ɗana ba ne? Ashe, shi ba ɗan gaban goshina ba ne? A duk lokacin da na ambace shi a kan muguntarsa Nakan tuna da shi da ƙauna. Saboda na ƙwallafa zuciyata a kansa, Hakika zan yi masa jinƙai, ni Ubangiji na faɗa.


To, ina so ku san irin yawan shan faman da nake yi dominku, da waɗanda suke a Lawudikiya, da kuma duk waɗanda ba su taɓa ganina ba.


Ya ku 'ya'yana ƙanana, ina sāke shan wahalar naƙudarku, har Almasihu ya siffatu a zuciyarku!


Abin nan da nake rubuto muku fa, ba ƙarya nake yi ba, a gaban Allah nake faɗa.


Ransa kuma yana a gare ku fiye da dā ƙwarai, duk sa'ad da yake tunawa da biyayyarku, ku duka, da kuma yadda kuka yi na'am da shi a cikin halin bangirma tare da matsananciyar kula.


Ai, ba wata rashin yarda a zuciyarmu, sai dai a taku.


Saboda tsananin jinƙai na Allahnmu, Daga Sama hasken asubahi zai ɓullo mana, Daga can Sama ne fa zai keto mana,


Ya Ubangiji, ka dube mu daga Sama, wurin da kake cike da tsarki da ɗaukaka. Ina kulawan nan da kake yi mana? Ina ikon nan naka? Ina ƙaunan nan taka da juyayin nan naka? Kada ka watsar da mu.


Na yi nishi da ɓacin zuciya a kan Mowab, na yi nishi da baƙin ciki saboda Kir-heres.


Duk kuwa wanda yake da abin hannunsa, yake kuma ganin ɗan'uwansa da rashi, sa'an nan ya rufe ido gare shi, ƙaƙa ƙaunar Allah yake zaune a cikinsa?


Ya ɗan'uwana, ka yarda in sami wata fa'ida a gare ka saboda Ubangiji! Ka sanyaya mini zuciya saboda Almasihu.


Yadda kuka sani, ba mu taɓa yin daɗin baki ko kwaɗayi ba. Allah kuwa shi ne shaida.


Saboda haka, sai ku ɗauki halin tausayi, da kirki, da tawali'u, da salihanci, da haƙuri, idan ku zaɓaɓɓu ne na Allah, tsarkaka, ƙaunatattu,


Yana begenku ku duka, har ma ya damu ƙwarai don kun ji ba shi da lafiya.


In akwai ƙarfafawa a cikin Almasihu, in dai da ƙarfin rinjaye na ƙauna, in har da tarayyarku ga Ruhu, da soyayyarku da kuma tausayinku,


Gama farin ciki muke yi in muna raunana, ku kuna ƙarfafa. Addu'armu ita ce ku kammala.


Akwai wani a Sama Wanda zai tsaya mini ya goyi bayana.


Domin dukanku 'ya'yan Allah ne, ta wurin bangaskiya ga Almasihu Yesu.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ