Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Farawa 49:18 - Littafi Mai Tsarki

18 Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

18 “Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Farawa 49:18
32 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ina sa zuciya ga cetonka ƙwarai, ya Ubangiji! Ina samun farin ciki ga dokarka.


Ina jiranka ka cece ni, ya Ubangiji, Ina aikata abin da ka umarta.


Amma ni zan kafa ido ga Ubangiji, Zan jira ceton Allahna, Allahna zai ji ni.


Sa'ad da wannan ya faru, kowa zai ce, “Shi Allahnmu ne! Mun dogara gare shi, ya kuwa cece mu. Shi ne Ubangiji. Mun dogara gare shi, yanzu kuwa muna da farin ciki domin ya cece mu!”


Na zaƙu, ina jiran taimako daga Ubangiji, Ga maganarsa na dogara.


ku kuma saurari komowar Ɗansa daga Sama, wanda ya tasa daga matattu, wato Yesu, mai kuɓutar da mu daga fushin nan mai zuwa.


To, akwai wani mutum a Urushalima, mai suna Saminu, adali, mai bautar Allah, yana kuma ɗokin ganin ta'aziyyar Isra'ila. Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.


Mala'ikan kuma ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.


Za ta haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, domin shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”


Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke sauraronsa, Da wanda suke nemansa kuma.


Ka ƙaunace mu da madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji, Ka taimake mu da cetonka.


Na yi ta jiran taimakon Ubangiji, Sa'an nan ya kasa kunne gare ni, ya ji kukana.


Ina addu'a matuƙa domin ceto ya zo ga Isra'ila daga Sihiyona! Sa'ad da Ubangiji ya sāke arzuta jama'arsa, Zuriyar Yakubu za su yi farin ciki, Jama'ar Isra'ila za su yi murna.


Gama mu, ta wurin ikon Ruhu, muke ɗokin cikar begen nan namu na samun adalcin Allah saboda bangaskiya.


In kuwa muna sa zuciya ga abin da ba mu samu ba, da jimiri mukan yi sauraronsa.


Ga shi, duk halitta tana marmari, tana ɗokin ganin bayyanar 'ya'yan Allah.


Shi kuwa dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba, yana kuwa sauraron bayyanar Mulkin Allah.


Yusufu ya zo, mutumin Arimatiya, wani ɗan majalisa mai mutunci, wanda shi ma yake sauraron bayyanar Mulkin Allah, ya yi ƙarfin hali ya shiga wurin Bilatus, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.


Zan yi ciniki da kai da sunan babban sarki, wato Sennakerib. Zan ba ka dawakai dubu biyu idan za ka iya samun yawan mutanen da za su hau su!


Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai. Muna sa zuciyarmu gare ka. Ka dinga kiyaye mu yau da gobe, ka kuma cece mu a lokatan wahala.


Ubangiji ya ɓoye kansa daga jama'arsa, amma ni na dogara gare shi, na kafa zuciyata a gare shi.


Kamar yadda bara yake dogara ga maigidansa, Baranya kuma ga uwargijiyarta, Haka nan muke zuba ido gare ka, ya Ubangiji Allahnmu, Har mu sami jinƙanka.


Ka nuna mini yawan ƙaunar da kake yi mini, ya Ubangiji, Ka cece ni bisa ga alkawarinka.


Ga Allah kaɗai na dogara, A gare shi na sa zuciyata.


Ga Allah kaɗai na dogara, Cetona daga gare shi yake fitowa.


Duk da haka dai, Ubangiji yana jira ya yi muku alheri. A shirye yake ya yi muku jinƙai, domin a kullum yana aikata abin da yake daidai. Ta wurin dogara ga Ubangiji ake samun farin ciki.


Dan zai zama maciji a gefen hanya, Zai zama kububuwa a gefen turba, Mai saran diddigen doki Don mahayin ya fāɗi da baya.


Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, Shi ne wanda ya cece ni. Wannan ne Allahna, zan yabe shi, Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.


Muguntar mugun takan kawo hallakarsa, amma adalin mutum, an kiyaye shi ta wurin dattakonsa.


Ubangiji ya ce, “Ɗan kasuwa wanda yake da ma'aunin algus a hannunsa. Yana jin daɗin yin zalunci.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ