Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Farawa 3:19 - Littafi Mai Tsarki

19 Za ka yi zuffa da aiki tuƙuru kafin ka sami abinci, har ka koma ƙasa, gama da ita aka siffata ka, kai turɓaya ne, ga turɓaya kuma za ka koma.” (2Tas 3.10; Far 2.7; Zab 90.3; 104.29; M.Had 12.7)

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

19 Da zuffan goshinka za ka ci abincinka har ka koma ga ƙasa, da yake daga cikinta aka yi ka. Gama kai turɓaya ne, kuma ga turɓaya za ka koma.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Farawa 3:19
33 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

sa'an nan turɓaya ta koma ƙasa kamar a dā, ruhu kuma ya koma wurin Allah wanda ya ba da shi.


Da duk mai rai ya halaka, Mutum kuma ya koma ƙura.


Sa'ad da ka rabu da su sukan tsorata, In ka zare numfashin da ka ba su, sai su mutu, Su koma turɓaya, da ma da ita aka yi su.


Sa'an nan Ubangiji Allah ya siffata mutum daga turɓayar ƙasa, a cikin kafafen hancinsa kuwa ya hura numfashin rai, mutum kuma ya zama rayayyen taliki.


Kakan sa mutane su koma yadda suke, Su zama ƙura.


Kada ɓarawo ya ƙara yin sata, a maimakon haka sai ya motsa jiki yana aikin gaskiya da hannunsa, har da zai sami abin da zai ba matalauta.


Dukansu wuri ɗaya za su tafi, gama dukansu biyu daga turɓaya suka fito, dukansu biyu kuma za su koma cikinta.


Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga shi, na jawo wa kaina in yi magana da Ubangiji, ni da nake ba kome ba ne, amma turɓaya ne da toka.


Waɗanda suka rasu za su tashi, waɗansu zuwa rai madawwami, waɗansu kuwa zuwa kunya da madawwamin ƙasƙanci.


Wace riba ce mutum zai samu daga cikin aikinsa, Da yake yi a duniya?


Maƙogwarona ya bushe kamar ƙura, Harshena kuma na liƙe wa dasashina na sama. Ka bar ni matacce cikin ƙura.


“Ni baƙo ne, ina tsakaninku, ina zaman baƙunci. Ku sayar mini da wurin yin makabarta, domin in binne matata, in daina ganinta!”


Ai, ko dā ma, sa'ad da muke a tare, mun yi muku wannan umarni, cewa duk wanda ya ƙi yin aiki, kada a ba shi abinci.


Ubangiji ya san abin da aka yi mu da shi, Yakan tuna, da ƙura aka yi mu.


Ya ku 'yan'uwa, kuna iya tunawa da wahala da famar da muka sha, har muna aiki dare da rana, don kada mu nauyaya wa kowane ɗayanku, duk sa'ad da muke yi muku bisharar Allah.


Mukan bar duniyan nan kamar yadda muka shigo ta, ba mu da kome. Dukan ayyukanmu, ba abin da za mu ɗauka mu tafi da shi.


Na ɗauri aniya in jarraba, in bincika dukan abubuwan da ake yi a duniyan nan. Allah ya ƙaddara mana abu mai wuya.


Mutuwa tana jiran wanda ya ƙi bin hanyar hankali.


Masu girmankai duka za su rusuna masa, 'Yan adam duka za su rusuna masa, Dukan waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa.


Amma duk abu guda ne su, mutuwa za su yi, a binne, Tsutsotsi su lulluɓe su duka.


Ko da yake ciwo ya riga ya cinye fatata, A wannan jiki zan ga Allah.


ya ce, “Ban shigo duniya da kome ba, ba kuma zan fita cikinta da kome ba. Ubangiji ya bayar, shi ne kuma ya karɓe, yabo ya tabbata ga sunansa.”


Mutumin farko daga ƙasa yake, na turɓaya ne. Na biyun kuwa daga Sama yake.


Tun da yake an ƙaddara wa ɗan adam ya mutu sau ɗaya ne, bayan haka kuma sai shari'a,


“Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za ta ba ka, za ka kuwa ci ganyayen saurar.


Ta ƙaƙa zai amince da talikinsa wanda aka yi da ƙasa, Abin da yake na ƙura, ana kuwa iya murƙushe shi kamar asu.


Sa'an nan mutane sukan fita su yi aikinsu, Su yi ta aiki har maraice ya yi.


Ba wani amfani a sha wahalar aiki saboda abinci, A yi asubancin tashi, a yi makarar kwanciya, Gama Ubangiji yakan hutar da waɗanda yake ƙauna.


Haka nan kuwa dukan kwanakin Adamu shekara ce ɗari tara da talatin, ya rasu.


Ka tuna, ya Allah, kai ka halicce ni, da yumɓu kuwa ka yi ni. Za ka murtsuke ni ne, in kuma koma ƙura?


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ