Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Farawa 19:29 - Littafi Mai Tsarki

29 Amma sa'ad da Allah ya hallaka biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya fid da Lutu daga halakar.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

29 Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Farawa 19:29
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ba saboda adalcinku, ko kuma gaskiyarku ne ya sa za ku shiga ƙasar, ku mallake ta ba, amma saboda muguntar waɗannan al'ummai ne, Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku domin kuma ya cika maganar da ya rantse wa kakanninku, wato su Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.


Allah kuwa ya tuna da Nuhu da dukan dabbobin gida da na jeji waɗanda suke cikin jirgi tare da shi. Allah ya sa iska ta hura bisa duniya, ruwaye suka janye.


Ka gafarta zunubaina da kurakuraina masu yawa na ƙuruciyata. Saboda madawwamiyar ƙaunarka da alherinka, Ka tuna da ni, ya Ubangiji!


da yake kuma ya ceci Lutu adali, wanda fajircin kangararru ya baƙanta masa rai ƙwarai


“Ƙaƙa zan iya rabuwa da ke, ya Ifraimu? Ƙaƙa zan miƙa ki, ya Isra'ila? Ƙaƙa zan maishe ki kamar Adma? Ƙaƙa zan yi da ke kamar Zeboyim? Zuciyata tana motsawa a cikina, Juyayina ya huru.


Yakan kiyaye dukan waɗanda suke ƙaunarsa, Amma zai hallaka mugaye duka.


Bai manta da mu sa'ad da aka yi nasara da mu ba, Gama ƙaunarsa madawwamiyar ce.


Ka tuna da ni sa'ad da za ka taimaki jama'arka, ya Ubangiji! Ka sa ni cikinsu, sa'ad da za ka cece su.


Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki Wanda ya yi wa bawansa Ibrahim.


Sai kuma na umarci Lawiyawa su tsarkake kansu, su yi tsaron ƙofofin don a kiyaye ranar Asabar da tsarki. “Ya Allahna, ka tuna da wannan aiki nawa, ka rayar da ni saboda girman madawwamiyar ƙaunarka.”


“Ka tuna da ni, ya Allahna, saboda wannan. Kada ka manta da ayyukan kirki da na yi a Haikalin Allah da kuma na hidimarsa.”


Allah kuwa ya tuna da Rahila, ya saurare ta, ya buɗe mahaifarta.


Zan kuwa maishe ka al'umma mai girma, zan sa maka albarka, in sa ka ka yi suna, domin ka zama sanadin albarka.


Zai cika alkawarinsa har abada, Alkawaransa kuma don dubban zamanai,


Yanzu dai waɗannan su ne zuriyar Tera, Tera ya haifi Abram, da Nahor, da Haran, Haran kuwa shi ne ya haifi Lutu.


Amma saboda Ubangiji ya ƙaunace ku, yana kuma so ya cika rantsuwar da ya yi wa kakanninku, shi ya sa ya fisshe ku da dantse mai iko ya fanshe ku kuma daga gidan bauta, wato daga ikon Fir'auna, Sarkin Masar.


Ka tuna da bayinka, su Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, kada ka kula da taurinkan jama'ar nan, ko muguntarsu, ko zunubansu


ko da mutum uku ɗin nan suna cikinta, ni Ubangiji Allah na rantse da zatina, ba za su ceci 'ya'ya mata ko 'ya'ya maza ba, su ne kaɗai za su tsira, amma ƙasa za ta zama kufai.


Muguntarka ta shafi mutum ne kamarka, Haka kuma adalcinka ya shafi ɗan adam ne kawai.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ