Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Farawa 1:3 - Littafi Mai Tsarki

3 Allah ya ce, “Bari haske ya kasance,” sai kuwa ya kasance.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Farawa 1:3
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Domin shi Allah wanda ya ce, “Haske yă ɓullo daga duhu ya haskaka,” shi ne ya haskaka zukatanmu domin a haskaka mutane su san ɗaukakarsa a fuskar Yesu Almasihu.


Haske na haskakawa cikin duhu, duhun kuwa bai rinjaye shi ba.


Ni na halicci haske duk da duhu, Ni ne na kawo albarka duk da la'ana. Ni Ubangiji, na yi dukkan waɗannan abu.


“Rana ba za ta ƙara zama haskenki da rana ba, Ko wata ya zama haskenki da dare. Ni, Ubangiji, zan zama madawwamin haskenki, Hasken ɗaukakata zai haskaka a kanki.


Wannan shi ne jawabin da muka ji a gunsa, muke sanar da ku cewa Allah haske ne, ba kuwa duhu gare shi ko kaɗan.


domin dā ku duhu ne, amma a yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi zaman mutanen haske,


Akwai hakikanin haske mai shigowa duniya da yake haskaka kowane mutum.


Hukuncin kuwa shi ne, haske ya shigo duniya, amma mutane suka fi ƙaunar duhu da hasken, don ayyukansu mugaye ne.


Ubangiji ya halicci duniya da umarninsa, Rana, da wata, da taurari kuma bisa ga maganarsa.


Bari su duka su yabi sunan Ubangiji! Ya umarta, sai suka kasance.


Haske yakan haskaka adalai, Haka kuma murna ta cika ga masu nagarta.


Da magana ya halicci duniya, Ta wurin umarninsa kowane abu ya bayyana.


Har wa yau sabon umarni nake rubuto muku, wanda yake tabbatacce ga Almasihu, da kuma gare ku, domin duhu yana shuɗewa, hakikanin haske kuma yana haskakawa.


Saboda haka aka ce, “Farka, ya kai mai barci, ka tashi daga matattu. Almasihu kuwa zai haskaka ka.”


Ka yi lulluɓi da haske. Ka shimfiɗa sammai kamar alfarwa.


“Ina hanya zuwa wurin da haske yake? A ina kuma duhu yake?


Shi ne kaɗai marar mutuwa, yake kuma zaune a cikin hasken da ba ya kusatuwa. Shi kuwa ba mutumin da ya taɓa ganinsa, ko kuwa zai iya ganinsa. Girma da madawwamin mulki su tabbata a gare shi. Amin, amin.


Ubangiji shi ne Allah, yana yi mana alheri, Ku ɗauki hadayunku ku yi ta idi, Ku ɗaura su a zankayen bagade.


Ga shi, yakan baza waƙiya kewaye da shi, Yakan rufe ƙwanƙolin duwatsu. Zurfin teku yana nan da duhunsa.


Da ya faɗi haka ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Li'azaru fito!”


Sai Yesu ya miƙa hannu, ya taɓa shi, ya ce, “Na yarda, ka tsarkaka.” Nan take kuturtarsa ta warke.


Waɗannan su ne asalin sama da duniya sa'ad da aka halicce su. A ranar da Ubangiji Allah ya yi duniya da sama,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ