Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ezra 8:17 - Littafi Mai Tsarki

17 Na kuma aike su zuwa wurin Iddo, shugaba a Kasifiya. Na faɗa musu abin da za su faɗa wa Iddo a Kasifiya da 'yan'uwansa ma'aikatan Haikali, wato ya aiko mana waɗanda za su yi hidima a Haikalin Allahnmu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

17 Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da ’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ezra 8:17
16 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ga lissafin ma'aikatan Haikali da suka komo. Zuriyar Ziha, da zuriyar Hasufa, da zuriyar Tabbawot Zuriyar Keros, da zuriyar Siyaha, da zuriyar Fadon Zuriyar Lebana, da zuriyar Hagaba, da zuriyar Akkub Zuriyar Hagab, da zuriyar Shamlai, da zuriyar Hanan Zuriyar Giddel, da zuriyar Gahar, da zuriyar Rewaiya Zuriyar Rezin, da zuriyar Nekoda, da zuriyar Gazam Zuriyar Ussa, da zuriyar Faseya, da zuriyar Besai Zuriyar Asna, da Me'uniyawa, da Nefushiyawa Zuriyar Bakbuk, da zuriyar Hakufa da zuriyar Harhur Zuriyar Bazlut, da zuriyar Mehida, da zuriyar Harsha Zuriyar Barkos, da zuriyar Sisera, da zuriyar Tema Zuriyar Neziya, da zuriyar Hatifa.


Wannan shi ya sa na bar ka a Karita, musamman domin ka ƙarasa daidaita al'amuran da suka saura, ka kuma kafa dattawan ikkilisiya a kowane gari, kamar yadda na nushe ka,


“Domin haka ga abin da ni, Ubangiji na ce, Idan ka komo sa'an nan zan kawo ka. Za ka tsaya a gabana. Idan ka hurta abin da yake gaskiya ba na ƙarya ba, Za ka zama kakakina. Za su komo gare ka, Amma kai ba za ka koma wurinsu ba.


Sa'an nan Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina, ya ce mini, “Ga shi, na sa maganata a bakinka.


A shekara ta bakwai kuma ta sarautar sarki Artashate, waɗansu mutanen Isra'ila, da waɗansu firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da matsaran ƙofa, da ma'aikatan Haikali, suka taho Urushalima.


Dukan zuriyar ma'aikatan Haikali da zuriyar barorin Sulemanu su ɗari uku da tasa'in da biyu ne.


Sa'an nan ya ce mata, “Ko akwai hannun Yowab cikin dukan sha'anin nan naki?” Ita kuwa ta amsa, “Na rantse da kai, ya ubangijina, sarki, ba dama a yi maka ƙumbiya-ƙumbiya. Haka ne, Yowab baranka ne ya sa ni. Shi ya sa dukan waɗannan magana a bakin baranyarka.


Sa'an nan ki tafi wurin sarki, ki ce masa haka.” Sai ya faɗa mata abin da za ta faɗa.


Zan tayar musu da wani annabi kamarka daga cikin 'yan'uwansu. Zan sa magana a bakinsa, zai faɗa musu duk abin da na umarce shi.


Ga shi, ni na ɗauki 'yan'uwanku, Lawiyawa, daga cikin mutanen Isra'ila. Kyauta suke a gare ku, waɗanda aka bayar ga Ubangiji don su lura da alfarwa ta sujada.


Sai ka yi magana da shi. Ka kuma sa masa maganata a baka, zan kuwa kasance tare da bakinka da bakinsa. Zan kuma sanar da ku abin da za ku yi.


Waɗanda suka fara zama a biranen mallakarsu, su ne Isra'ilawa da firistoci, da Lawiyawa, da kuma ma'aikatan Haikali.


Sai na sa a kirawo Eliyezer, da Ariyel, da Shemaiya, da Elnatan, da Yarib, da Elnatan, da Natan, da Zakariya, da Mehullam waɗanda suke shugabanni, a kuma kirawo Yoyarib da Elnatan masu hikima.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ