Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ezekiyel 7:16 - Littafi Mai Tsarki

16 Idan akwai waɗanda suka tsere, za a same su a kan duwatsu kamar kurciyoyin kwaruruka, suna baƙin ciki dukansu, kowa yana baƙin ciki saboda laifinsa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

16 Duk waɗanda suka tsira suka tsere za su kasance a cikin duwatsu, suna kuka kamar kurciyoyin kwaruruka, kowanne saboda zunubansa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ezekiyel 7:16
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Dukanmu muna gurnani kamar beyar, muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci, amma ina. Muna ta neman ceto, amma ya yi nisa da mu.


Muryata ƙarama ce, ba kuma ƙarfi, Na kuwa yi kuka kamar kurciya, Idanuna sun gaji saboda duban sama. Ya Ubangiji, ka cece ni daga dukan wannan wahala.


Ya Ubangiji Allah na Isra'ila, kai mai adalci ne, gama ka bar mana ringin da ya tsira kamar yadda yake a yau. Ga mu nan gabanka da zunubinmu, gama ba wanda zai iya tsayawa a gabanka saboda wannan.”


Su da suka tsira daga al'ummar Yahuza za su yi lafiya kamar dashe-dashen da saiwoyinsu suka shiga da zurfi cikin ƙasa, suka kuma ba da amfani.


Sa'an nan za ku tuna da mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau. Za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda muguntarku da ayyukanku na banƙyama.


‘Yan kaɗan ne za su tsere wa takobi, za su kuwa koma daga ƙasar Masar zuwa ƙasar Yahuza. Sauran mutanen Yahuza da suka ragu, waɗanda suka zo Masar da zama, za su sani ko maganar wa za ta cika, tasu ko kuwa tawa.


Ba waɗansu daga cikin mutanen Yahuza da suka ragu, waɗanda suka zo Masar da zama, da za su tsere ko su rayu. Ba wani daga cikinsu da zai koma Yahuza inda suke marmarin komawa da zama, ba wanda zai koma, sai dai 'yan gudun hijira.”


Da kuka za su komo. Da ta'aziyya zan bishe su, in komar da su, Zan sa su yi tafiya a gefen rafuffukan ruwa, A kan miƙaƙƙiyar hanya, inda ba za su yi tuntuɓe ba. Gama ni uba ne ga Isra'ila, Ifraimu kuwa ɗan farina ne.”


Da a ce Ubangiji Mai Runduna bai rage sauran jama'a ba, da an hallakar da Urushalima gaba ɗaya, kamar yadda aka yi wa Saduma da Gwamrata.


Ka saurare ni, ka amsa mini, Gama damuwata ta gajiyar da ni tiƙis.


“Gama ana jin muryar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Ga yadda muka lalace! Aka kunyatar da mu ɗungum! Don mun bar ƙasar, domin sun rurrushe wuraren zamanmu.’ ”


Idan kuwa waɗansu sun wanzu daga cikinta suka fita da 'ya'yansu mata da maza zuwa wurinta, za ka ga halinsu da ayyukansu, za ka tabbata, masifar da na aukar wa Urushalima, ba kawai ba ne.


Tumakina sun watse, suna yawo a kan dukan duwatsu da tuddai, sun warwatsu a duniya duka, ba wanda zai nemo su.’


An tsiraita sarauniya, an tafi da ita, 'Yan matanta suna makoki, suna kuka kamar kurciyoyi, Suna bugun ƙirjinsu.


Babbar ranar Ubangiji ta gabato, Tana gabatowa da sauri. Ku ji muryar ranar Ubangiji! Jarumi zai yi kuka mai zafi.


“Gama laifofinmu sun yi yawa a gabanka, zunubanmu kuwa suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu suna tare da mu, muna kuwa sane da laifofinmu,


An ji murya a kan filayen tuddai, Kūka da roƙo ne na 'ya'yan Isra'ila maza, Domin sun rabu da hanyarsu, Sun manta da Ubangiji Allahnsu.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ