Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Esta 6:6 - Littafi Mai Tsarki

6 Da shigowar Haman, sai sarki ya ce masa, “Me za a yi wa mutumin da sarki yake so ya ɗaukaka?” Haman ya yi tunani ya ce a ransa, “Wane ne sarki yake so ya ɗaukaka, in banda ni?”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

6 Sa’an nan Haman ya shigo, sai sarki ya ce masa, “Me ya kamata a yi wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama?” Haman dai ya yi tunani a ransa ya ce, “Wane ne sarki zai girmama in ba ni ba?”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Esta 6:6
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Girmankanki ya yaudare ki, Kina zaune a kagara, a kan dutse, Wurin zamanki yana can ƙwanƙolin duwatsu. Don haka a zuciya kike cewa, ‘Wa zai saukar da ni ƙasa?’


Girmankai jagora ne zuwa ga hallaka, fāriya kuwa zuwa ga fāɗuwa.


domin kowa yă girmama Ɗan, kamar yadda ake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan, ba ya girmama Uban da ya aiko shi ke nan.


Sai aka ji wata murya daga Sama ta ce, “Wannan shi ne Ɗana ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi ƙwarai.”


Zan ji daɗin yi musu alheri. Zan dasa su a wannan ƙasa da aminci da zuciya ɗaya.”


Ubangiji ya ce, “Ga bawana, wanda na ƙarfafa, Wanda na zaɓa, wanda nake jin daɗinsa. Na cika shi da ikona, Zai kuwa kawo shari'ar gaskiya ga dukan al'ummai.


Ba wanda za a girmama sai mai tawali'u, mutum mai girmankai kuwa yana kan hanyar hallaka.


Marasa sani sukan mutu saboda ba su yarda da hikima ba. Wawaye kuwa sukan hallaka saboda rashin kulawarsu.


Ka sa waɗanda suke murna da kuɓutata Su yi ta sowa ta murna, suna cewa, “Ubangiji mai girma ne! Yana murna da cin nasarar bawansa!”


Haman kuwa ya ɗauki rigunan da dokin. Ya sa wa Mordekai riguna, ya hawar da shi kan dokin, ya zagaya da shi a dandalin birnin, yana cewa, “Haka za a yi wa wanda sarki yake so ya ɗaukaka.”


Sa'an nan a ba ɗaya daga cikin manyan sarakunanka rigunan ya sa wa wanda kake so ka ɗaukaka, ya kuma hawa da shi kan dokin, sa'an nan ya zagaya da shi a dandalin birni, yana shelar a gabansa yana cewa, ‘Haka za a yi wa wanda sarki yake so ya ɗaukaka.’ ”


Sai Haman ya ce wa sarki, “Abin da za a yi wa wanda sarki yake so ya ɗaukaka ke nan.


Ya faɗa musu darajar wadatarsa, da yawan 'ya'yansa, da yawan matsayin da sarki ya girmama shi da su, da yadda sarki ya ciyar da shi gaba fiye da sarakuna da barorin sarki.


Akwai waɗansu mutane da suke yi wa jama'a ƙallon raini suna ɗaurin gira.


Barorin sarki suka ce, “Ai, Haman ne yake tsaye a shirayi.” Sai sarki ya ce ya shigo.


Sarki ya ce, “Bisa ga doka, me za a yi da sarauniya Bashti da yake ba ta yi biyayya da umarnin da na aika ta hannun babani ba?”


wanda ya gayyato ku duka biyu kuma yă zo ya ce maka, ‘Ba mutumin nan wuri.’ Sa'an nan a kunyace ka koma mazauni mafi ƙasƙanci.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ