Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayyukan Manzanni 9:41 - Littafi Mai Tsarki

41 Ya kuwa miƙa mata hannu ya tashe ta. Sai ya kira tsarkaka da matan waɗanda mazansu suka mutu ya miƙa musu ita rayayyiya.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

41 Ya kama ta a hannu ya taimake ta ta tsaya a ƙafafunta. Sa’an nan ya kira masu bi da kuma gwaurayen ya miƙa musu ita da rai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayyukan Manzanni 9:41
15 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

To, a kwanakin nan da yawan masu bi suke Ƙaruwa, sai Yahudawa masu jin Helenanci suka yi wa Ibraniyawa gunaguni domin bā a kula da matayensu waɗanda mazansu suka mutu, a wajen rabon gudunmawa a kowace rana.


Sai ya matso, ya kama hannunta, ya tashe ta, zazzaɓin kuwa ya sake ta, har ta yi musu hidima.


Sai suka tafi da saurayin nan a raye, daɗin da suka ji kuwa ba kaɗan ba ne.


Sai Bitrus ya kama hannunsa na dama, ya tashe shi. Nan tāke ƙafafunsa da wuyan sawunsa suka yi ƙarfi.


Mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuwa ya ba da shi ga uwa tasa.


Ya kusaci ƙofar garin ke nan, sai ga wani mamaci ana ɗauke da shi, shi kaɗai ne wajen uwa tasa, mijinta kuwa ya mutu. Mutanen gari da yawa sun rako ta.


Yakan kiyaye baƙi waɗanda suke zaune a ƙasar. Yakan taimaki gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu. Yakan lalatar da dabarun mugaye.


Waɗanda suke bakin mutuwa sukan sa mini albarka, Na taimaki gwaurayen da mazansu suka mutu, Su raira waƙa don murna.


Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga soro, ya kai shi cikin gida, ya ba uwar. Ya ce mata, “Ki gani, ɗanki yana da rai.”


Suka ce masa, “Har yanzu Yusufu yana nan da rai, shi ne kuwa mai mulki bisa ƙasar Masar duka.” Sai gabansa ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.


Amma Hananiya ya amsa ya ce, “Ya Ubangiji, na sha jin labarin mutumin nan gun mutane da yawa, kan yawan muguntar da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima.


To, da Bitrus ya zazzaga lardi duka, sai kuma ya je wurin tsarkakan nan da suke zaune a Lidda.


Ka girmama gwauraye mata, waɗanda ba sa da mataimaka.


Gwauruwa marar mataimaki kuwa, mai zaman kaɗaici, ta dogara ga Allah ke nan, tana nacewa ga roƙon Allah, tana addu'a dare da rana.


Sa'an nan ya ce, “Ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu, ya ɗauka.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ