Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayyukan Manzanni 25:10 - Littafi Mai Tsarki

10 Amma Bulus ya ce, “Ai, a tsaye nake a majalisar Kaisar, a inda ya kamata a yi mini shari'a. Ban yi wa Yahudawa wani laifi ba, kai kanka kuwa ka san da haka sarai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

10 Bulus ya amsa ya ce, “Yanzu ina tsaye a gaban kotun Kaisar, inda ya kamata a yi mini shari’a. Ban yi wani laifi ga Yahudawa ba, kai da kanka ma ka san da haka sarai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayyukan Manzanni 25:10
12 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ba ruwanmu da ɓoye-ɓoye na munafunci, ko makirci, ko yi wa Maganar Allah algus, amma ta wurin bayyana gaskiya a fili, sai kowane mutum ya shaidi gaskiyarmu a lamirinsa a gaban Allah.


Su kuwa da suka tuhume ni, suna so su sake ni, don ban yi wani laifi da ya isa kisa ba.


Bayan sun keɓe waje ɗaya, suka yi shawara, suka ce, “Ai, mutumin nan bai yi wani abin da ya isa kisa ko ɗauri ba.”


Amma ni ban ga abin da ya yi wanda ya isa kisa ba. Tun da kuma shi kansa ya nema a mai da shari'arsa a gaban Augustas, ƙudura in aika da shi zuwa wurinsa.


Don ya sani saboda hassada ne suka bashe shi.


Saboda haka, da suka zo nan tare, ban yi wani jinkiri ba, sai kawai na hau gadon shari'a kashegari, na kuma yi umarni a kawo mutumin.


Bai fi kwana takwas ko goma a wurinsu ba, sai ya tafi Kaisariya. Kashegari kuma ya zauna a kan gadon shari'a, ya yi umarni a zo da Bulus.


Na kuwa tarar suna zarginsa a kan maganar Shari'arsu, amma laifin da suka ɗora masa bai kai ga kisa ko ɗauri ba.


Banda haka kuma, a lokacin da yake zaune a kan gadon shari'a, sai mata tasa ta aiko masa da cewa, “Ka fita daga sha'anin mara laifin nan, don yau na sha wahala ƙwarai a mafarkinsa.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ