Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 9:15 - Littafi Mai Tsarki

15 Ko da yake ba ni da laifi, Duk da haka iyakar abin da zan iya yi ke nan, In roƙi Allah ya yi mini jinƙai, Shi da yake alƙalina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 9:15
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Da cewa na yi zunubi, na shiga uku ke nan a wurinka. Amma sa'ad da na yi abin kirki ba na samun yabo. Ina baƙin ciki ƙwarai, kunya ta rufe ni.


Amma sai ka juyo ka yi roƙo ga Allah Maɗaukaki.


Da aka zage shi bai rama ba, da ya sha wuya kuma bai yi kashedi ba, sai dai ya dogara ga mai shari'ar adalci.


Sa'ad da ka yi addu'a zai amsa maka, Za ka kuwa kiyaye alkawaran da ka yi.


Kada ka hukunta ni, ya Allah. Ka faɗa mini laifin da kake tuhumata da shi.


“In da ni ne kai, da sai in juya wurin Allah, In kai ƙarata a wurinsa.


Ban sani ina da wani laifi ba, amma ba don wannan na kuɓuta ba, ai, Ubangiji shi ne mai gwada ni.


Ya Allahna, ka karkato kunnenka ka ji, ka buɗe idanunka ka ga yadda mu da birnin da ake kira da sunanka muka lalace. Ba cewa muna da wani adalci na kanmu shi ya sa muka kawo roƙe-roƙenmu ba, amma saboda yawan jinƙanka.


Sai na mai da hankalina wajen Ubangiji Allah, ina nemansa ta wurin addu'a, da roƙe-roƙe tare da azumi, ina saye da tufafin makoki, na zauna cikin toka.


Da kuka za su komo. Da ta'aziyya zan bishe su, in komar da su, Zan sa su yi tafiya a gefen rafuffukan ruwa, A kan miƙaƙƙiyar hanya, inda ba za su yi tuntuɓe ba. Gama ni uba ne ga Isra'ila, Ifraimu kuwa ɗan farina ne.”


Ina da aminci, zan faɗa wa Allah ra'ayina, Zai tabbatar da amincina duka.


Sa'ad da ya yi addu'a gare shi, Allah ya karɓi roƙonsa da hurwarsa, ya sāke komar da shi Urushalima da mulkinsa. Sa'an nan ne Manassa ya sani Ubangiji shi ne Allah.


Amma duk da haka ko ya yardar mini in yi magana ma, Ban yi tsammani zai saurare ni ba.


Ni ba ni da laifin kome, amintacce ne ni, A kunne sai a ji kalmomina kamar na marar gaskiya ne. Kowane abu da na fāɗa, kā da ni yake yi.


Ba ni da laifin kome, amma ba na ƙara damuwa. Na gaji da rayuwa.


Ai, na riga na yi magana sau ɗaya, har ma sau biyu, Ba zan amsa ba, ba zan ƙara cewa kome ba.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ