Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 8:13 - Littafi Mai Tsarki

13 Marasa tsoron Allah kamar iwan nan suke, Ba su da sa zuciya muddin sun rabu da Allah.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 8:13
25 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Mutuwa ce maƙarar dukan mugaye, Da dukan waɗanda suke ƙin Allah.


Mai yiwuwa ne ƙarfin halina ya cece ni, Tun da yake ba wani mugun mutumin da zai iya zuwa gaban Allah.


Amma mugaye za su dudduba ko'ina da fid da zuciya, Ba su da wata hanyar da za su kuɓuta. Sauraronsu kaɗai shi ne mutuwa.”


Abin da mutanen kirki suke sa zuciya yakan kai su ga murna, amma mugaye ba su da wani abu da za su sa zuciya a kai.


Marasa tsoron Allah ba za su sami zuriya ba, Wuta za ta cinye gidajen da aka gina da dukiyar rashawa.


Mugaye sukan gamu da faɗuwarsu, ba magāda, amma iyalan adalai sukan dawwama.


“Ku ji wannan ku da kuke ƙyale ni, In ba haka ba zan hallaka ku, Ba wanda zai cece ku.


Ba wani mugun mutum wanda ya taɓa daɗewa da farin ciki.


Idan kun manta da Ubangiji Allahnku, kuka bi gumaka, kuka bauta musu, kuka yi musu sujada, to, yau ina faɗakar da ku, cewa lalle za ku hallaka


yă farfasa masa jiki da bulala, ya ba shi rabonsa tare da munafukai. Nan za a yi kuka da cizon baki.”


Sai na ce, “Darajata ta ƙare, Ba ni kuma da sa zuciya wurin Ubangiji.”


Kuna mantawa da Ubangiji wanda ya halicce ku, Wanda ya shimfiɗa sammai, Ya kuma kafa harsashin ginin duniya? Don me za ku yi ta jin tsoron fushin waɗanda suke zaluntarku, Da waɗanda suke shiri su hallaka ku? Fushinsu ba zai taɓa yi muku kome ba!


Jama'ar Sihiyona cike da zunubi suke, suna ta rawar jiki don tsoro. Suka ce, “Hukuncin Allah kamar wuta ce mai ci har abada. Akwai wani daga cikinmu da zai iya tsira daga irin wannan wuta?”


Mugun mutum da girmankansa yana cewa, “Ba Allah!” Wannan ne abin da mugu yake tunani.


“Waɗanda ba su da tsoron Allah a zuciyarsu, Suna tanada wa kansu fushi, Ba su neman taimako sa'ad da ya ɗaure su.


Dā yana zaune lafiya, Sai razana ta tatike shi, Ta jawo shi zuwa ga Sarkin Mutuwa.


to, sai ku lura, kada ku ɗaukaka kanku, har ku manta da Ubangiji Allahnku wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, wato inda kuka yi bauta.


“Ku kula fa, don kada ku manta da Ubangiji Allahnku, ku ƙi kiyaye umarnansa, da farillansa, da dokokinsa waɗanda na umarce ku da su yau.


to, kada ku manta da Ubangiji wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.


In ruwan ta ƙafe, ita ce za ta fara bushewa, Tun tana ƙanƙana ba ta isa a yanke a yi amfani da ita ba.


Sa'ad da mugaye suka ga wannan, Sai suka tunzura, suka harare shi da fushi, suka ɓace, Sa zuciyarsu ta ƙare har abada.


Mugun mutum yakan mutu da burinsa. Dogara ga dukiya bai amfana kome ba.


Amma mugaye ba haka suke ba, Su kamar yayi suke wanda iska take kwashewa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ