Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 7:16 - Littafi Mai Tsarki

16 Na fid da zuciya. Na gaji da rayuwa. Ku rabu da ni. Rayuwa ba ta da wata ma'ana.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 7:16
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Na gaji da rayuwa, Ku ji ina fama da baƙin ciki.


Iliya ya yi tafiyarsa yini guda cikin jeji, ya tafi ya zauna a gindin wani itace ya yi roƙo domin ya mutu, yana cewa, “Yanzu ya isa haka, ya Ubangiji, ka karɓi raina, gama ban fi kakannina ba.”


A sa'ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro. Yunusa ya ji kamar zai suma saboda zafin rana da take bugun kansa. Sai ya so ya mutu, ya ce, “Gara in mutu da ina zaune da rai.”


Ka ƙyale ni ko zan sami kwanciyar rai, Kafin in tafi, ai, tawa ta ƙāre.”


Ka kawar da fuska daga gare shi, ka rabu da shi, Ka bar shi ya ji daɗin kwanakinsa na fama da aiki idan zai iya.


Raina bai kusa ƙarewa ba? A bar ni kawai! Bari in ci moriyar lokacin da ya rage mini.


Ba ni da laifin kome, amma ba na ƙara damuwa. Na gaji da rayuwa.


Da ma ya ci gaba kawai ya kashe ni, Ko ya sake ikonsa ya datse ni!


Domin haka fa, ya Ubangiji, ina roƙonka ka ɗauki raina, gama yanzu gara in mutu da in zauna da rai.”


Shi kamar hucin iska yake, Kwanakinsa kuwa kamar inuwa mai wucewa ne.


Ta haka ya ƙare kwanakinsu kamar fitar numfashi, Bala'i ya aukar wa rayukansu farat ɗaya.


Talakawa kamar shaƙar numfashi suke, Manyan mutane, su ma haka suke marasa amfani. Ko an auna su a ma'auni, sam ba su da nauyin kome, Sun fi numfashi shakaf.


Kada ka ƙara hukunta ni! Na kusa mutuwa saboda bugun da kake yi mini!


Rifkatu kuwa ta ce wa Ishaku, “Na gaji da raina saboda matan Hittiyawa. Idan Yakubu zai auri ɗaya daga cikin waɗannan mata na Hittiyawa, wato daga matan ƙasar, wane amfani raina zai daɗa mini?”


“Ka tuna, ya Ubangiji, raina iska ne kawai, Farin cikina ya riga ya ƙare.


Har nakan fi so a rataye ni, Gara in mutu da in rayu a wannan hali.


Yakan tuna su mutane ne kawai, Kamar iskar da take hurawa ta wuce.


Sauran mutanen muguwar tsaran nan waɗanda suke a wuraren da na warwatsa su, za su fi son mutuwa fiye da rayuwa. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”


Bai kuma fi inuwa ba! Duk abin da yake yi banza ne, Yakan tara dukiya, amma bai san wanda zai more ta ba!


Saboda haka rai ba wani abu ba ne a gare ni, domin dukan abin da yake cikinsa bai kawo mini kome ba sai wahala. Duka banza ne, ba abin da nake yi sai harbin iska kawai.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ