Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 6:9 - Littafi Mai Tsarki

9 Da ma ya ci gaba kawai ya kashe ni, Ko ya sake ikonsa ya datse ni!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 6:9
16 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Iliya ya yi tafiyarsa yini guda cikin jeji, ya tafi ya zauna a gindin wani itace ya yi roƙo domin ya mutu, yana cewa, “Yanzu ya isa haka, ya Ubangiji, ka karɓi raina, gama ban fi kakannina ba.”


Domin haka fa, ya Ubangiji, ina roƙonka ka ɗauki raina, gama yanzu gara in mutu da in zauna da rai.”


A sa'ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro. Yunusa ya ji kamar zai suma saboda zafin rana da take bugun kansa. Sai ya so ya mutu, ya ce, “Gara in mutu da ina zaune da rai.”


A waɗannan kwanaki kuwa mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su same ta ba, za su ƙagauta su mutu, mutuwa kuwa sai ta guje musu.


Ka hukunta ni dare da rana, ya Ubangiji, Ƙarfina duka ya ƙare sarai, Kamar yadda laima yake bushewa, Saboda zafin bazara.


Ku abokaina ne! Ku ji tausayina! Ikon Allah ya fyaɗa ni ƙasa.


“Ya Allah, da ma a ce ka ɓoye ni a lahira, Ka bar ni a ɓoye, har fushinka ya huce, Sa'an nan ka sa lokacin da za ka tuna da ni!


“Me ya sa Allah ya ƙi ba ni abin da nake roƙo? Me ya sa ya ƙi yin abin da nake so?


Ba ni da laifin kome, amma ba na ƙara damuwa. Na gaji da rayuwa.


“Na gaji da rayuwa, Ku ji ina fama da baƙin ciki.


Amma mugaye za su dudduba ko'ina da fid da zuciya, Ba su da wata hanyar da za su kuɓuta. Sauraronsu kaɗai shi ne mutuwa.”


An datse raina, ya ƙare, Kamar alfarwar da aka kwance, Kamar saƙar da aka yanke, Na zaci Allah zai kashe ni.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ