Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 5:15 - Littafi Mai Tsarki

15 Amma Allah yakan ceci matalauta daga mutuwa, Yakan kuma ceci masu bukata daga zalunci.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 5:15
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Da zuciya ɗaya zan ce wa Ubangiji, “Ba wani kamarka! Kakan kāre marasa ƙarfi daga masu ƙarfi, Talaka da matalauci kuma daga azzalumai!”


Na sani kai, ya Ubangiji, kana kāre matsalar talakawa, Da hakkin matalauta.


Saboda yakan kāre talaka, Domin ya cece shi daga waɗanda Suka sa masa laifin mutuwa.


Ya tsamo masu bukata daga cikin baƙin cikinsu, Ya sa iyalansu su riɓaɓɓanya kamar garkunan tumaki.


Ka sa sarki ya yi wa talakawa shari'ar gaskiya, Ya taimaki waɗanda suke da bukata, Ya kuma hukunta azzalumai!


Za ka saurara ga addu'o'in masu kaɗaici, ya Ubangiji, Za ka ba su ƙarfin hali.


Amma kana gani, kana kuma lura da masu shan wuya, da masu ɓacin rai, Koyaushe kuma a shirye kake ka yi taimako. Mutum wanda ba shi da mai taimako yakan danka kansa gare ka, Gama kullum kakan taimaki masu bukata.


Mugaye sukan yi ruri suna gurnani kamar zakoki, Amma Allah yakan sa su yi tsit, Ya kakkarya haƙoransu.


Kamar zakoki da ba su da abin da za su kashe su ci, Haka nan za su mutu, 'ya'yansu kuwa su warwatse duka.


Allah yakan kuɓutar da kai daga ƙarairayi da ɓata suna, Yakan cece ka daga hallaka.


Nakan karya muƙamuƙin marar adalci, In sa yă saki ganimar da yă kama.


Suka sa matalauta su yi kuka ga Allah, Ya kuwa ji kukan waɗanda ake tsananta wa.


Bai kamata marar tsoron Allah ya yi mulki ba, Don kada ya tura jama'a cikin tarko.


Ba ya rayar da masu laifi, Amma yakan ba waɗanda ake tsananta wa halaliyarsu.


Zai kuɓutar da waɗanda suke shan tsanani, Ta wurin tsananin da suke sha, Yakan buɗe kunnuwansu ta wurin shan wahala.


Akan hana wa mugaye haske, Sa'ad da sukan ɗaga hannuwansu sama akan kakkarya su.


Sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya yi wa Nebuzaradan shugaban matsara umarni a kan Irmiya ya ce,


Allah kuwa ya sa Daniyel ya sami farin jini da soyayya a wurin sarkin fāda.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ