Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 4:3 - Littafi Mai Tsarki

3 Ka koya wa mutane da yawa, Ka kuma ƙarfafa hannuwan marasa ƙarfi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 4:3
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ku ƙarfafa hannuwan da suka gaji, Da gwiwoyin da suke fama da rashin ƙarfi.


Domin wannan, ku miƙe hannuwanku da suke reto, da gwiwoyinku marasa ƙarfi.


Ni kuwa na yi maka addu'a, kada bangaskiyarka ta kāsa. Kai kuma, bayan da ka juyo, sai ka ƙarfafa 'yan'uwanka.”


Kalmomin mutumin kirki za su amfani mutane da yawa, amma kana iya hallaka kanka da wauta.


Da sai in ba ka shawara ta ƙarfafawa, In yi ta yi maka maganar ta'azantarwa.


Kada wata alfasha ta fita daga bakinku, sai dai irin maganar da ta kyautu domin ingantawa, a kuma yi ta a kan kari, domin ta sa alheri ga masu jinta.


[Sai wani mala'ika ya bayyana a gare shi daga Sama, yana ƙarfafa shi.


Amma ka umarci Joshuwa, ka ƙarfafa shi. Shi ne zai jagorar jama'ar nan, su haye, shi ne kuma wanda zai rarraba musu gādon ƙasar da za ka gani.’


“Kun karya zuciyar adali ta wurin ƙaryarku, ko da yake ni ban karya zuciyarsa ba. Kun ƙarfafa wa mugu gwiwa, don kada ya bar hanyarsa ta mugunta, ya tsira.


Ubangiji ya koya mini abin da zan faɗa, Domin in iya ƙarfafa marar ƙarfi. A kowace safiya yakan sa in yi marmarin jin abin da zai koya mini.


Mutum mai hikima, wanda ya isa mutum, akan san shi ta wurin haziƙancinsa, kamar yadda kalmominsa suke da daɗi, haka ma rinjayarsa take.


Mutane masu hikima suke yaɗa ilimi, amma banda wawaye.


Gama na zaɓe shi don ya umarci 'ya'yansa da gidansa domin su kiyaye tafarkin Ubangiji a bayansa, su riƙe adalci da shari'a.” Ubangiji ya tabbatar wa Ibrahim da abin da ya alkawarta masa.


A kullum maganarku ta zama mai ƙayatarwa, mai daɗin ji, domin ku san irin amsar da ta dace ku ba kowa.


Suka kuma kiyaye idin abinci marar yisti kwana bakwai da murna, gama Ubangiji ya sa su yi murna, ya kuma juyo da zuciyar Sarkin Assuriya wajensu, saboda haka ya taimake su da aikin Haikalin Allah, Allah na Isra'ila.


Idan wani ya yi tuntuɓe, Ya gaji, ya rasa ƙarfi, Kalmominka suka ƙarfafa zuciyarsa, Har ya iya tsayawa kyam.


Waɗanda suka ji labarina sukan sa mini albarka, Waɗanda suka gan ni sukan yi na'am da ni.


Ni ne idon makafi, guragu kuma, ni ne ƙafarsu.


Ni mahaifi ne ga matalauta, Nakan bincika don in warware al'amarin da ya dami baƙi.


Mutane sukan kasa kunne su jira, su yi shiru Sa'ad da nake ba da shawara.


A wannan rana za a ce wa Urushalima, “Kada ki ji tsoro, ke Sihiyona, Kada ki bar hannuwanki su raunana.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ