Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 39:11 - Littafi Mai Tsarki

11 Za ka dogara gare shi saboda tsananin ƙarfinsa? Za ka kuma bar masa aikinka?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 39:11
16 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

A maimakon haka sai kuka shirya ku tsere wa maƙiyanku a kan dawakai masu gudu. Daidai ne, tilas ku tsere! Tsammani kuke saurin gudun dawakanku ya isa, amma waɗanda za su fafare ku sun fi ku gudu!


Wannan shi ne jawabin da Allah ya yi a kan dabbobin da suke kudancin hamada, “Jakadu sun yi tafiya a ƙasa mai hatsari, inda zakoki suke, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke. Suna labta wa jakunansu da raƙumansu kayayyaki masu tsada da za su kai gaisuwa ga al'ummar da ba za ta taimake su da kome ba.


Idan ba ka da shanun noma ba za ka sami hatsi mai yawa ba, amma idan kana da su za ka sami hatsi mai yawan gaske.


Ba ya jin daɗin ƙarfafan dawakai, Ba ya murna da jarumawan mayaƙa.


Ka sa shanunmu su hayayyafa, Kada su yi ɓari ko su ɓace. Ka sa kada a ji kukan damuwa a kan titunanmu!


Waɗansu ga karusan yaƙinsu suke dogara, Waɗansu kuwa ga dawakansu, Amma mu, ga ikon Ubangiji Allahnmu muke dogara!


Suka labta wa jakunansu hatsi, suka tashi.


Kowace dabba ta duniya, da kowane tsuntsu na sararin sama, da kowane mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifaye na teku, za su riƙa jin tsoronku suna fargaba. An ba da su a hannunku.


Allah kuwa ya sa musu albarka, ya ce musu, “Ku hayayyafa ku riɓaɓɓanya, ku cika duniya, ku yi iko da ita, ku mallaki kifayen teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma dukan abin da yake da rai da yake kai da kawowa cikin duniya.”


Allah kuma ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, da kamanninmu, su mallaki kifayen da suke a cikin teku, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobi, da dukan duniya, da kowane abu mai rarrafe da yake rarrafe bisa ƙasa.”


“Wannan ne ƙarshen allolin Babila! Dā ana yi wa Bel da Nebo sujada, Amma yanzu ana labtunsu a kan jakuna, Sun zama nawaya a kan dabbobin da suka gaji!


Ka iya ɗaure shi da igiya a kwarin kunya? Ko kuwa zai yi maka kaftu a fadamarka?


Ka gaskata zai komo, Ya kawo maka hatsi a masussukarka?


Allah ne ya fisshe shi daga Masar, Ya yi yaƙi dominsu kamar kutunkun ɓauna.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ