Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 37:23 - Littafi Mai Tsarki

23 Mai Iko Dukka, ya fi ƙarfin ganewarmu, Shi mai girma ne, da iko, da gaskiya, Da yalwataccen adalci, Ba ya garari.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 37:23
38 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Shi ne kaɗai marar mutuwa, yake kuma zaune a cikin hasken da ba ya kusatuwa. Shi kuwa ba mutumin da ya taɓa ganinsa, ko kuwa zai iya ganinsa. Girma da madawwamin mulki su tabbata a gare shi. Amin, amin.


Zurfin hikimar Allah da na saninsa da rashin iyaka suke! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban bincikewa, hanyoyinsa kuma sun fi gaban bin diddigi!


Maɗaukaki kana ƙaunar abin da yake daidai, Ka kawo adalci cikin Isra'ila, Ka kawo adalci da gaskiya.


“Ga shi kuwa, Allah Mai Girma, ba ya raina kowa, Shi mai girma ne, mai cikakkiyar basira.


Allah mai hikima ne, mai iko, Ba wanda zai iya ja in ja da shi.


Ni Ubangiji Allah na ce ba na murna da mutuwar kowa, saboda haka sai ku tuba domin ku rayu.”


Ni Ubangiji Allah, na ce, ina jin daɗin mutuwar mugu ne? Ban fi so ya bar mugun halinsa ya rayu ba?


daga dukan wahalar da suke sha. Ba mala'ika ne ya cece su ba, amma Ubangiji ne. Da ƙaunarsa da juyayinsa ya fanshe su. A koyaushe yake lura da su a dā,


Ku zo ku gabatar da matsalarku a ɗakin shari'a, Bari waɗanda aka kai ƙara su yi shawara da juna. Wane ne ya faɗi abin da zai faru, Ya kuma yi annabci tuntuni? Ashe, ba ni ba ne, Ubangiji, Allah wanda ya ceci mutanensa? Ba wani Allah sai ni.


Fushinsa ba ya daɗewa, Alherinsa kuwa har matuƙa ne. Mai yiwuwa ne yă zama ana kuka da dare, Amma a yi murna da safe.


“Kana iya gane matuƙa da iyakar Girman Allah da na ikonsa?


Su kam, sun hore mu a ɗan lokaci kaɗan don ganin damarsu, amma shi, don amfanin kanmu ne yake horonmu, domin mu zama abokan tarayya a cikin tsarkinsa.


Kowane abu Ubana ne ya mallaka mini. Ba kuwa wanda ya san ko wane ne Ɗan sai dai Uban, ko kuma ya san ko wane ne Uban sai dai Ɗan, da kuma wanda Ɗan yake so ya bayyana wa.”


Kada ka kai mu wurin jaraba, Amma ka cece mu daga Mugun.’


Shi ya sa wa kowane abu lokacinsa. Shi ne kuma ya sa mana buri mu san abin da yake nan gaba, amma fa bai ba mu cikakken sanin ayyukan da yake yi ba, tun daga farko har zuwa ƙarshe.


Ubangiji sarki ne! Yana saye da ɗaukaka, suturarsa ƙarfi ne. Hakika duniya ta kahu sosai a inda take, Ba kuwa za ta jijjigu ba.


Ku faɗa wa Allah cewa, “Al'amuran da kake aikatawa Suna da banmamaki ƙwarai! Ikonka yana da girma ƙwarai, Har maƙiyanka sukan durƙusa a gabanka don tsoro.


Ka kakkafa duwatsu ta wurin ikonka, Ka bayyana ƙarfin ikonka.


Sau ɗaya Allah ya faɗa, Sau biyu na ji, cewa Allah yake da iko.


Ka koya mana abin da za mu faɗa masa, Ba za mu iya gabatar da ƙararrakinmu ba, gama mu dolaye ne.


Ga shi kuwa, Allah Maɗaukaki ne, Ba mu kuwa san iyakar ɗaukakarsa ba, Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.


Amma waɗannan kaɗan ne kawai daga cikin al'amuransa. Ɗan ƙis kaɗai muke ji a kansa. Amma wa zai iya fahimtar ikon tsawarsa?”


In gwada ƙarfi ne? To, a iya gwada wa Allah ƙarfi? In kai shi ƙara ne? Wa zai sa shi ya je?


Allah bai taɓa yin danniya ba, Bai kuma taɓa fāsa aikata abin da yake daidai ba.


Sararin sama ba shi ne matuƙa a wurin Allah ba, Amma ga shi, yana can nesa da kai, Allah ya san lahira, Amma kai ba ka sani ba.


“Allah mai iko ne, duka sai a ji tsoronsa, A samaniya yake tafiya da mulkinsa da salama.


Zan tattaro ilimina daga nesa, In bayyana adalcin Mahaliccina.


Daga arewa wani haske kamar na zinariya ya fito mai banmamaki, Allah yana saye da ɗaukaka mai bantsoro.


Wane ne zai iya sanin gaibi? Abin ya yi mana zurfi ƙwarai, yana da wuyar ganewa.


Ka faɗa musu, ni Ubangiji Allah, na ce, ‘Hakika, ba na murna da mutuwar mugu, amma na fi so mugun ya bar hanyarsa ya rayu. Ku juyo, ku juyo daga mugayen hanyoyinku, gama don me za ku mutu, ya mutanen Isra'ila?’


Madawwamiyar ƙauna, ta Ubangiji ce. Kai kanka, ya Ubangiji, kake sāka wa Kowane mutum bisa ga ayyukansa.


Ubangiji mai girma ne, dole ne a fifita yabonsa, Girmansa ya fi ƙarfin ganewa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ