Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 36:6 - Littafi Mai Tsarki

6 Ba ya rayar da masu laifi, Amma yakan ba waɗanda ake tsananta wa halaliyarsu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 36:6
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Na sani kai, ya Ubangiji, kana kāre matsalar talakawa, Da hakkin matalauta.


Amma Allah yakan ceci matalauta daga mutuwa, Yakan kuma ceci masu bukata daga zalunci.


ashe kuwa, Ubangiji ya san yadda zai kuɓutar da masu tsoronsa daga gwaje-gwaje, ya kuma tsare marasa adalci a kan jiran hukunci, har ya zuwa ranar shari'a,


Zai yi wa matalauta shari'a daidai. Zai kuma kāre hakkin masu tawali'u. Bisa ga umarninsa za a hukunta ƙasar, Mugaye za su mutu.


Ka sa sarki ya yi wa talakawa shari'ar gaskiya, Ya taimaki waɗanda suke da bukata, Ya kuma hukunta azzalumai!


Amma kai, ya Allah, za ka jefar da masu kisankai, da maƙaryata can ƙasa cikin zurfafa, Kafin su kai rabin kwanakinsu a duniya. Amma ni, zan dogara gare ka.


Allah yana tunawa da waɗanda suke shan wuya, Ba ya mantawa da kukansu, Yana kuma hukunta waɗanda suke cutarsu.


A ranar da Allah ya yi fushi, ya yi hukunci, A kullum mugun ne kaɗai yakan kuɓuta.


Amma zai sa maƙiyanka su sha kunya, Za a shafe gidajen mugaye.”


“Yanzu fa sai ka yi tunani. Ka faɗi bala'i ɗaya wanda ya taɓa fāɗa wa adalin mutum.


Yakan buge su a gaban mutane saboda muguntarsu,


Da gari ya waye, Ka kawar da muguntar da ake yi da dare?


Hakika adalai za su yabe ka, Za su zauna a gabanka.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ