Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 34:29 - Littafi Mai Tsarki

29 Idan Allah zai yi shiru, da wa zai sa wa wani laifi? Idan ya ɓoye fuskarsa, wa zai iya ganinsa, Ko aka yi wa al'umma ko ga mutum?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 34:29
26 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kai kake ba da cikakkiyar salama, ya Ubangiji, Ga waɗanda suke riƙe da manufarsu da ƙarfi, Waɗanda suke dogara gare ka.


“Bai taɓa sākewa ba. Ba wanda zai iya gāba da shi, Ko kuma ya hana shi yin abin da yake so ya aikata.


Na bar ku da salama. Salamata nake ba ku. Ba kamar yadda duniya take bayarwa nake ba ku ba. Kada ku damu, kada kuma ku ji tsoro.


Gama kowa zai yi abin da yake daidai, za a sami salama da zaman lafiya har abada.


Kada ka ɓoye mini fuskarka, ya Ubangiji! Kada ka yi fushi da ni, Kada kuwa ka kori bawanka. Kai ne kake taimakona, tun dā ma, Kada ka bar ni, kada ka yashe ni, Ya Allahna, Mai Cetona!


Ta haka salamar Allah, wadda ta fi gaban dukkan fahimta, za ta tsai da zukatanku da tunaninku ga Almasihu Yesu.


“ ‘Amma idan wata al'umma ko wani mulki bai yarda ya bauta wa Nebukadnezzar, Sarkin Babila ba, bai kuma ɗaura karkiyar Sarkin Babila a wuyansa ba, zan hukunta wa wannan al'umma da takobi, da yunwa, da annoba, har in hallaka ta, ta hannun Nebukadnezzar, ni Ubangiji na faɗa.


Yanzu ka amsa mini, ya Ubangiji! Na fid da zuciya duka! Kada ka ɓuya mini, Don kada in zama cikin waɗanda suke gangarawa zuwa lahira.


Kana yi mini alheri, ya Ubangiji, Ka kiyaye ni kamar a kagarar dutse. Amma sa'ad da ka ɓoye mini fuskarka, Sai in cika da tsoro.


Har yaushe za ka manta da ni, ya Ubangiji? Har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye mini fuskarka?


Sa'ad da Allah ya rurrushe, wa zai iya sāke ginawa? Wa kuma zai iya fitar da mutumin da Allah ya sa a kurkuku?


Sa'ad da sarki yake zaune a gidansa, Ubangiji kuma ya hutasshe shi daga fitinar abokan gābansa da suke kewaye da shi,


Suka sa matalauta su yi kuka ga Allah, Ya kuwa ji kukan waɗanda ake tsananta wa.


Bai kamata marar tsoron Allah ya yi mulki ba, Don kada ya tura jama'a cikin tarko.


Don ka ba shi hutawa a kwanakin wahala, Kafin a haƙa wa mugaye kabari.


Ubangiji kuwa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma hutashe ka.”


Mulkin Yehoshafat kuwa ya sami salama, gama Allahnsa ya ba shi hutawa a kowane gefe.


Shi ne yake shugabancin sauran al'umma, ba zai hukunta su ba? Shi ne yake koya wa dukan mutane, shi ba shi da sani ne?


Ni kaina zan yi kiwon tumakin, in ba su hutawa, ni Ubangiji Allah na faɗa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ