Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 33:13 - Littafi Mai Tsarki

13 Me ya sa kake yi wa Allah gunaguni, Cewa ba ya karɓar maganarka ko ɗaya?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 33:13
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Mai neman sa wa wani laifi ya jā da Mai Iko Dukka? Wanda yake gardama da Allah, bari ya ba da amsa.”


Ko tukunyar yumɓu tana iya gardama da magininta, Tukunyar da take daidai da sauran tukwane? Ko yumɓu ya iya tambayar abin da maginin yake yi? Ko tukunya tana iya gunaguni a kan magininta?


Ashe, har mā tsokani Ubangiji ya yi kishi? Mun fi shi ƙarfi ne?


“Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji? Ko kuwa wa ya taɓa ba shi wata shawara?”


amma in na Allah ne, ba dama ku rushe su. Kada fa a same ku kuna gāba da Allah.”


Ya ce musu, “Sanin lokatai da zamanai, da Uba ya sa cikin ikonsa, ba naku ba ne.


Ashe, ba ni da ikon yin abin da na ga dama da abin da yake mallakata? Ko kuwa kana jin haushin alherina ne?’


Dukan mazaunan duniya ba a bakin kome suke a gare shi ba. Yakan yi yadda ya nufa da rundunar sama da mazaunan duniya, Ba mai hana shi, ba kuma mai ce masa, ‘Me kake yi?’


Zuciyarka za ta iya ɗaurewa, hannuwanka kuma za su ƙarfafa a ranar da zan gamu da kai? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata.


Na kafa miki tarko, ya kuwa kama ki, ya Babila, Ke kuwa ba ki sani ba. An same ki, an kama, Domin kin yi gāba da ni.”


Tun da farko na faɗa muku yadda abin zai zama, Tuntuni na yi faɗi a kan abin da zai faru. Na kuwa ce shirye-shiryena ba za su taɓa fāɗuwa ba, Zan aikata dukan abin da na yi niyyar yi.


Sau ɗaya Allah ya faɗa, Sau biyu na ji, cewa Allah yake da iko.


To, ƙaƙa zan yi in samo kalmomin da zan amsa wa Allah?


“Sanin gaibu na Ubangiji Allahnmu ne, amma abubuwan da aka bayyana namu ne, mu da 'ya'yanmu har abada, don mu kiyaye dukan maganar dokokin nan.”


Ya kai ɗan adam! Wane ne kai har da za ka yi jayayya da Allah? Ashe, abin da aka gina zai iya ce wa magininsa, “Don me ka yi ni haka?”


“Kana iya gane matuƙa da iyakar Girman Allah da na ikonsa?


Yakan ɗauki abin da yake so, ba wanda yake hana shi, Ba wanda yake tambayarsa cewa, ‘Me kake yi?’


Kada ka hukunta ni, ya Allah. Ka faɗa mini laifin da kake tuhumata da shi.


In haka ne, me ya sa kake bin diddigin dukan laifofina, Kana farautar dukan abin da na yi?


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ