Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 32:13 - Littafi Mai Tsarki

13 Ku lura kada ku ce kuna da hikima, Allah ne kaɗai yake da iko ya kā da shi, ba mutum ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

13 Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 32:13
23 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji ya ce, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa, kada mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa, kada kuma mawadaci ya yi fariya da wadatarsa.


Kada kowa yă ruɗi kansa. In waninku ya zaci shi mai hikima ne, yadda duniya ta ɗauki hikima, sai yă mai da kansa marar hikima, domin ya sami zama mai hikima.


Yesu ya amsa masa ya ce, “Ba ka da wani iko a kaina in ba an ba ka daga Sama ba, saboda haka wanda ya bāshe ni gare ka ya fi ka zunubi.”


“Ubangiji zai fara ba mutanen Yahuza nasara, domin kada darajar jama'ar Dawuda da ta mazaunan Urushalima ta fi ta mutanen Yahuza.


Lalle ka fi Daniyel hikima, Ba asirin da yake ɓoye a gare ka.


Yanzu ne kaɗai nake sawa su faru, Ba wani abu makamancin wannan da ya faru a baya. Da ya faru, da za ku ɗauka cewa kun san kome a kansa.


Tuntuni na yi faɗi a kan makomarku, Na hurta abubuwa tun kafin su faru, Domin kada ku ɗauka cewa gumakanku ne suka yi su, Siffofinku ne kuma suka sa abin ya zama haka.


Kun shiga uku! A tsammaninku ku masu hikima ne, masu wayo ƙwarai.


Ku abokaina ne! Ku ji tausayina! Ikon Allah ya fyaɗa ni ƙasa.


Ba ku iya ganin abin da Allah ya yi mini, Ya kafa tarko don ya kama ni.


“Aha! Ashe, kai ne muryar jama'a, Idan ka mutu hikima ta mutu ke nan tare da kai.


Allah Maɗaukaki ya harbe ni da kibau, Dafinsu kuwa ya ratsa jikina. Allah ya jera mini abubuwa masu banrazana.


A cikin fushinsa Allah yakan hallaka su kamar hadiri.


Ayuba ya amsa, ya ce mata, “Wace irin maganar gāɓanci ce haka? Lokacin da Allah ya aiko mana da alheri, mukan yi na'am da shi, to, me zai sa sa'ad da ya aiko mana da wahala za mu yi gunaguni?” Cikin dukan wahalar da Ayuba ya sha, bai sa wa Allah laifi ba.


ya ce, “Ban shigo duniya da kome ba, ba kuma zan fita cikinta da kome ba. Ubangiji ya bayar, shi ne kuma ya karɓe, yabo ya tabbata ga sunansa.”


Ubangiji kuwa ya ce wa Gidiyon, “Mutanen da suke tare da kai sun yi yawa da zan ba da Madayanawa a hannunsu, kada ya zama Isra'ilawa su yi mini fāriya, su ce, ‘Ƙarfinmu ne ya cece mu.’


cewa ba zan ɗauki ko da zare ɗaya ko maɗaurin takalmi ba, ko kowane abin da yake naka, domin kada ka ce, ‘Na arzuta Abram.’


Ka sa ƙayayuwa su tsiro maimakon alkama, Tsire-tsire marasa amfani kuma maimakon sha'ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.


Na kasa kunne gare ku sosai, Amma ko ɗaya ba wanda ya kā da Ayuba. Ba kuma wanda ya ba shi amsar tambayarsa.


Ba da ni Ayuba yake magana ba, Saboda haka ba zan amsa masa da irin amsarku ba.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ