Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 31:14 - Littafi Mai Tsarki

14 To, wace amsa zan ba Allah sa'ad da ya tashi don ya hukuntar? Me zan iya faɗa sa'ad da Allah ya zo yi mini shari'a?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 31:14
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Gama Shari'a marar jinƙai ce ga wanda ba ya nuna jinƙai. Amma jinƙai yana rinjayar hukunci.


To, mun sani duk abin da Shari'a ta ce, ya shafi waɗanda suke ƙarƙashinta ne, don a tuƙe hanzarin kowa, duk duniya kuma tă sani ƙarƙashin hukuncin Allah take.


Bari dukan 'yan adam su yi tsit a gaban Ubangiji, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.


Mutumin kirkinsu kamar ƙaya yake, Mai gaskiyarsu kuwa kamar shingen ƙaya yake. Ranar da kuka sa mai tsaro, A ran nan za a aukar muku da hukunci. Yanzu ruɗewarku ta zo,


Ranar hukunci ta zo, ranar ramako ta iso, Isra'ila za ta sani! An ce annabi wawa ne, Mutumin da yake da ruhu kuwa mahaukaci ne, Saboda yawan muguntarku da ƙiyayyarku.


Me za ku yi sa'ad Allah zai hukunta ku? Me za ku yi kuma sa'ad da ya kawo muku masifa daga wata ƙasa mai nisa? Ina za ku sheƙa neman taimako? A ina kuma za ku ɓoye dukiyarku?


Ni bawanka, kada ka gabatar da ni a gaban shari'a, Gama ba wanda ba shi da laifi a gare ka.


Sa'ad da ka tashi domin ka yanke hukunci, Domin ka ceci waɗanda ake zalunta a duniya.


Hakika ka gane, Domin ka san asirin tunanin mutane.


Ka zo, ya Ubangiji! Kada ka bari mutane su gagare ka! Ka kawo arna a gabanka, ka hukunta su.


Allah yana tunawa da waɗanda suke shan wuya, Ba ya mantawa da kukansu, Yana kuma hukunta waɗanda suke cutarsu.


Ka tashi da fushinka, ya Ubangiji, Ka kuma tashi ka yi gāba da hasalar abokan gābana! Ka tashi, ka taimake ni, gama adalci kake so a yi.


Kada ka hukunta ni, ya Allah. Ka faɗa mini laifin da kake tuhumata da shi.


Da a ce Allah mutum ne, Da sai in mayar masa da magana, Da sai mun je ɗakin shari'a a yanka mana shari'a.


suka lura waɗansu almajiransa na cin abinci da hannuwa marasa tsarki, wato marasa wanki.


“Idan a ce ban kasa kunne ga kukan barorina mata da maza ba, Sa'ad da suka kawo koke-kokensu a kaina,


Ashe, shi wanda ya halicce ni a cikin mahaifa, Ba shi ne ya halicce su ba? Shi wanda ya siffata mu a cikin mahaifa?


Kada ka mallake shi da tsanani, amma ka ji tsoron Allahnka.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ