Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 30:16 - Littafi Mai Tsarki

16 “Yanzu zuciyata ta narke Kwanakin wahala sun same ni.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 30:16
8 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zuciyata takan ɓaci in na tuna da abin da ya wuce, Sa'ad da nakan tafi tare da taron jama'a zuwa Haikalin Allah, Ina bishe su a jere. Taron jama'a masu farin ciki, suna raira waƙa, Suna ta da murya, suna yabon Allah.


Ƙarfina ya ƙare, Ya rabu da ni kamar ruwan da ya zube ƙasa. Dukan gaɓoɓina sun guggulle, Zuciyata ta narke kamar narkakken kakin zuma.


Saboda haka zan ba shi matsayi mai girma, Matsayi a cikin manyan mutane masu iko. Da yardarsa ya ba da ransa Ya ɗauki rabon masu laifi. Ya maye gurbin masu zunubi da yawa, Ya kuwa sha hukuncin da ya cancanci masu zunubi. Ya yi roƙo dominsu.”


Wahalai iri iri sun kewaye ni, har ba su ƙidayuwa! Alhakin zunubaina ya tarar da ni, Har ba na iya gani, Sun fi gashin kaina yawa, na karaya.


A maimakon cin abinci, sai baƙin ciki nake yi, Ba kuma zan daina yin nishi ba,


Hannatu kuwa ta amsa ta ce, “Ba haka ba, ya shugabana, ni mace ce da take baƙin ciki ƙwarai. Ni ban sha ruwan inabi, ko wani abu mai sa maye ba, amma ina faɗa wa Ubangiji dukan abin da yake a zuciyata.


Suna yi wa uwayensu kuka, suna cewa, “Ina abinci da ruwan inabi?” Suna suma kamar mutanen da aka yi wa rauni A titunan birnin, Suna mutuwa a ƙirjin uwayensu.


Maƙogwarona ya bushe kamar ƙura, Harshena kuma na liƙe wa dasashina na sama. Ka bar ni matacce cikin ƙura.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ