Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 22:9 - Littafi Mai Tsarki

9 Ba ƙin taimako kaɗai ka yi ba, Amma har marayu ma ka yi musu ƙwace, ka wulakanta su.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 22:9
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Haka yake samun wanda ya wulakanta gwauraye. Bai kuma nuna alheri ga matan da ba su haihu ba.


Sukan saci jakunan marayu, Su kama san gwauruwa, Su ce sai ta biya basusuwanta.


A cikinka ana raina mahaifi da mahaifiya, ana kuma tsananta wa baƙo, ana cin zalin marayu, da gwauruwa, wato wadda mijinta ya mutu.


Ta haka kuke hana wa talakawa hakkinsu, kuna kuma ƙin yi musu shari'ar gaskiya. Ta haka kuke ƙwace dukiyar gwauraye, wato matan da mazansu suka rasu, da ta marayu.


Ko na ɗaga hannuna don in cuci maraya, Don na ga ina da kafar kuɓuta,


Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan zo wurinku domin in yi shari'a. Nan da nan zan tabbatar da laifin masu yin sihiri, da na mazinata, da na masu shaidar zur, da na masu zaluntar ma'aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu, da baƙi, da waɗanda ba su ganin girmana.”


Ubangiji Allah kuma ya ce, “Ina gāba da Fir'auna, Sarkin Masar, zan karya hannuwansa duka biyu, da lafiyayyen da kuma wanda na riga na karya. Zan sa takobinsa ya faɗi daga hannunsa.


Shugabanninku 'yan tawaye ne, abokan ɓarayi, a koyaushe sai karɓar kyautai suke yi, da rashawa. Amma ba su taɓa kare marayu a ɗakin shari'a, ko su kasa kunne ga ƙarar da gwauraye suka kawo ba, wato matan da mazansu suka mutu.


Ku koyi yin abin da yake daidai. Ku ga an aikata adalci, ku taimaki waɗanda ake zalunta, ku ba marayu hakkinsu, ku kāre gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu.”


Suna karkashe gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu, Da kuma baƙin da suke zaune a ƙasarmu.


Gama Ubangiji zai raba mugaye da ƙarfinsu, Amma zai kiyaye mutanen kirki.


Ka karya ikon mugaye, masu mugunta, Ka hukunta su saboda muguntarsu, Har hukuncinsu ya cika sarai.


“ ‘La'ananne ne wanda ya yi wa baƙo, ko maraya, ko gwauruwa ta gaske shari'a ta rashin gaskiya.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’


Kukan jefa wa bayi da marayu kuri'a, Kukan arzuta kanku daga abokanku na kurkusa.


An karye ikon Mowab da ƙarfinta, ni Ubangiji na faɗa.


[Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan ci kayan matan da mazansu sun mutu, kukan yi doguwar addu'a don ɓad da sawu. Saboda haka za a yi muku hukunci mafi tsanani.]


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ