Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 21:30 - Littafi Mai Tsarki

30 A ranar da Allah ya yi fushi, ya yi hukunci, A kullum mugun ne kaɗai yakan kuɓuta.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 21:30
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kowane abu da Ubangiji ya yi yana da makoma, makomar mugun kuwa hallaka ce.


Ta maganar Allah ne kuma sama da ƙasa da suke a nan a yanzu, aka tanada su ga wuta, ana ajiye su, har ya zuwa ranar nan da za a yi wa marasa bin Allah shari'a, a hallaka su.


Amma ga shi, saboda ƙeƙasasshiyar zuciyarka marar tuba, kana nema wa kanka fushin Allah a ranar fushi, sa'ad da za a bayyana hukuncin Allah macancani.


Dukan dukiyarsa za a hallaka ta a rigyawar fushin Allah.


don babbar ranar fushinsu ta zo, wa kuwa zai iya jure mata?”


Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu kai da kawowa, waɗanda aka tanada wa matsanancin duhu har abada.


Wannan rana ta hasala ce, Ranar azaba da wahala, Ranar lalatarwa da hallakarwa, Ranar duhu baƙi ƙirin, Ranar gizagizai da baƙin duhu,


Ubangiji Allah mai kishi ne, mai sakayya, Ubangiji mai sakayya ne, mai hasala. Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan maƙiyansa. Yana tanada wa maƙiyansa fushi.


Dukiya ba ta da wani amfani a ranar mutuwa, amma adalci zai hana ka mutuwa.


Ubangiji yana damanka, Zai kori sarakuna a ranar da ya husata.


“Amma daɗai Allah ba zai rabu da amintattu ba, Ba kuwa zai taɓa taimakon mugun mutum ba.


“Wannan ita ce ƙaddarar mugaye, Wadda Allah ya ƙayyade musu.”


“An taɓa kashe hasken mugun mutum? Ko masifa ta taɓa fāɗa wa wani daga cikinsu? Allah ya taɓa hukunta wa mugu da fushi,


Bari dai a hukunta masu zunubi Su kuma ga hasalar Allah.


“Ashe, ba ku yi magana da matafiya ba? Ba ku kuma san rahoton da suka kawo ba?


Ba wanda zai fito fili ya zargi mugun, Ko ya mayar masa da martani.


Yakan aika da masifa da lalacewa Ga waɗanda suke aikata abin da ba daidai ba.


Ka kwararar da rigyawar fushinka, Ka dubi dukan wanda yake alfarma, a wulakance.


Amma Isma'ilu ɗan Netaniya tare da mutum takwas suka tsere suka gudu zuwa wurin Ammonawa.


Sai Joshuwa ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu, ku rufe bakin kogon, sa'an nan ku sa mutane su yi tsaronsu.


Ba su shan wahala yadda sauran mutane suke sha, Ba su da wahala kamar sauran mutane,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ