Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 20:15 - Littafi Mai Tsarki

15 Mugun mutum yakan harar da dukiyar da ya samu ta hanyar zamba, Allah zai karɓe ta har da wadda ya ci a cikin cikinsa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 20:15
12 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Za ka harar da abin da ka ci, dukan daɗin bakinka zai tafi a banza.


Tilas 'ya'yansa maza su biya zambar da ya yi wa matalauta, Tilas hannuwansa su biya dukiyar da ya ƙwace.


Amma a cikinsa wannan abinci yakan zama da ɗaci, Ɗacinsa kamar na kowane irin dafi mai ɗaci ne.


Tilas ya rabu da dukan abin da ya yi wahalarsa. Ba dama ya mori dukiyarsa,


“Har abada ba zai kai ga samun abin da yake wahala ba.


Dukan dukiyarsa za a hallaka ta a rigyawar fushin Allah.


Ka sa waɗanda suke binsa bashi su kwashe Dukan abin da yake da shi. Ka sa baƙi su kwashe dukan abin da ya sha wahalar nema.


Mutane masu hikima suna zaune da wadata da nishaɗi, amma wawaye da zarar sun sami kuɗi sukan kashe su nan da nan.


Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya cinye Urushalima, Ya ragargaza ta, Ya maishe ta kufai, Ya haɗiye ta kamar yadda dodon ruwa yakan yi, Ya cika cikinsa da kayan marmarinta, Ya tatse ta sarai.


“Ai, waɗannan duka za su yi ta yi masa zambo, Su yi masa dariya ta raini, Su ce, ‘Tasa ta ƙare, shi wanda ya tattara abin da ba nasa ba, Har yaushe zai riƙa arzuta kansa ta hanyar ba da rance?’


Zan hukunta Bel, gunkin Babila, Zan sa ya yi aman abin da ya haɗiye, Ƙasashen duniya ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Garun Babila ya rushe!”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ