Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 20:10 - Littafi Mai Tsarki

10 Tilas 'ya'yansa maza su biya zambar da ya yi wa matalauta, Tilas hannuwansa su biya dukiyar da ya ƙwace.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

10 Dole ’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 20:10
15 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Tilas ya rabu da dukan abin da ya yi wahalarsa. Ba dama ya mori dukiyarsa,


Sai Zakka ya miƙe, ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ka ga, rabin mallakata zan ba gajiyayyu. Kowa na zalunta kuwa, zan mayar masa da ninki huɗu.”


Mai mulki wanda yake zaluntar talakawa, ya zama kamar ruwa mai lalatar da amfanin gona.


duk da haka in an kama shi, sai ya biya diyya sau bakwai, tilas kuwa ya ba da dukan abin da yake da shi.


Ka sa 'ya'yansa su rasa gidan zama, su riƙa yawon bara. Ka sa a kore su daga kufan da suke zaune!


Ko kaɗan, 'ya'yansu maza ba za su taɓa zama lafiya ba. Ba wanda zai tsaya musu a ɗakin shari'a.


Sai kuma ya biya diyyar 'yar tunkiya riɓi huɗu, domin ya aikata mugun abu na rashin tausayi.”


sai dai ko in gari ya riga ya waye. Dole ɓarawon ya yi cikakkiyar ramuwa, in kuwa ba shi da abin biya, a sayar da shi a biya abin da ya satar.


“Idan mutum ya saci sa ko tunkiya, ya yanka ko ya sayar, zai biya shanu biyar a maimakon sa, tumaki huɗu maimakon tunkiya.


Ubangiji ya sa jama'a su yi farin jini a wurin Masarawa, saboda haka Masarawa suka ba su abin da suka roƙa. Ta haka suka washe Masarawa.


Amma idan ka ƙi sakinsu, wato kana ta riƙonsu,


Kamar zakoki da ba su da abin da za su kashe su ci, Haka nan za su mutu, 'ya'yansu kuwa su warwatse duka.


Mugun mutum yakan harar da dukiyar da ya samu ta hanyar zamba, Allah zai karɓe ta har da wadda ya ci a cikin cikinsa.


Idan 'ya'yansu sun riɓaɓɓanya za su zama rabon takobi, Zuriyarsu kuwa ba za su sami isasshen abinci ba.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ