Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 18:21 - Littafi Mai Tsarki

21 Wannan ita ce ƙaddarar mugaye, Wannan ita ce ƙaddarar mutane waɗanda ba su damu da kome na Allah ba.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 18:21
16 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji ya ce, “Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, Ƙarya ce take rinjayar gaskiya a ƙasar. Suna ta cin gaba da aikata mugunta, Ba su kuwa san ni ba.


Suna cewa sun san Allah, amma suna sāɓa masa ta wurin aikinsu. Abin ƙyama ne su, kangararru, ko kaɗan ba su da wani amfani a wajen yin aiki nagari.


yana ta sāka wa waɗanda suke ƙi sanin Allah, da kuma waɗanda suka ƙi bin bisharar Ubangijinmu Yesu.


ba ta muguwar sha'awa ba, yadda al'ummai suke yi, waɗanda ba su san Allah ba.


Ka kwarara hasalarka a kan sauran al'umma da ba su san ka ba, Da a kan jama'ar da ba su kiran sunanka, Gama sun cinye Yakubu, Sun cinye shi, sun haɗiye shi, Sun kuma mai da wurin zamansa kufai.”


Dukan tsarar Joshuwa sun rasu, waɗanda suke tasowa kuwa suka manta da Ubangiji da abubuwan da ya yi wa Isra'ila.


Tun da yake sun ƙi su yarda su san Allah, Allah ya sallama su ga halin banza, su aikata abin kunya.


Ka yi fushi da al'umman da ba su yi maka sujada, Ka yi fushi da jama'ar da suka ƙi ka!


Kuna ta tambaya, ‘Ina ne gidan babban mutumin nan yanzu, Wato mutumin da yake aikata mugunta?’


Mugaye sukan ce wa Allah ya ƙyale su kurum, Ba su so su san nufinsa game da hanyoyinsu.


“Kai kuwa ɗana Sulemanu, sai ka san Allah na tsohonka, ka bauta masa da zuciya ɗaya, da kuma yardar rai, gama Ubangiji mai binciken dukan zukata ne, ya kuma san kowane irin nufi da tunani. Idan ka neme shi, za ka same shi, in kuwa ka rabu da shi, shi ma zai yi watsi da kai har abada.


'Ya'yan Eli, maza kuwa, ba su da kirki, ba su kula da Ubangiji ba,


Amma Fir'auna ya ce, “Wane ne Ubangiji, har da zan ji maganarsa, in bar Isra'ilawa su tafi? Ai, ban san Ubangiji ɗin nan ba, balle in bar Isra'ilawa su tafi.”


Duk abin da ya mallaka an ɗauke, Duk da haka ya mutu cikin rashin hikima.’ ”


“Wannan ita ce ƙaddarar mugaye, Wadda Allah ya ƙayyade musu.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ