Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 16:4 - Littafi Mai Tsarki

4 In da a ce a matsayina kake, ni kuma ina a naka, Ina iya faɗar duk abin da kake faɗa yanzu. Da sai in kaɗa kaina da hikima, In dulmuyar da kai a cikin rigyawar maganganu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 16:4
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sa'ad da mutane suka gan ni sun yi mini ba'a, Suna kaɗa kai saboda raini.


Duk wanda ya gan ni Sai yă maishe ni abin dariya, Suna zunɗena da harshensu suna kaɗa kai.


Dukan masu wucewa suna yin miki tafin raini. Suna yi wa Urushalima tsāki, Suna kaɗa mata kai, suna cewa, “Ai, Urushalima ke nan, Birnin nan da ake cewa mai cikakken jamali, Wanda ya ƙayatar da dukan duniya?”


Sun mai da ƙasarsu abar banƙyama, Abin raini har abada. Duk wanda ya wuce ta wurin zai razana ya kaɗa kansa.


Ubangiji ya ce, “Birnin Urushalima ya yi maka dariya, kai Sennakerib, yana yi maka ba'a.


Ta haka, in wata gaɓa ta ji ciwo, duk sai su ji ciwo tare, in kuwa an yabi wata, duk sai su yi farin ciki tare.


Ku taya masu farin ciki farin ciki, masu kuka kuwa ku taya su kuka.


Saboda haka duk abin da kuke so mutane su yi muku, ku ma sai ku yi musu, domin wannan shi ne Attaura da koyarwar annabawa.”


Wannan shi ne birnin da yake da harka, mai zaman lafiya, Wanda yake ce wa kansa, “Ba wani sai ni.” Ga shi, ya zama kufai, Wurin zaman dabbobi! Duk wanda ya wuce ta wurin, Zai yi tsaki, ya kaɗa kai.


Wawa ya cika yawan surutu. Wa ya san abin da zai faru nan gaba? Wa zai iya faɗa masa abin da zai faru bayan rasuwarsa?


Bisa ga yawan surutunka, mai yiwuwa ne ƙwarai ka yi zunubi, amma idan kai mai la'akari ne, sai ka yi shiru.


Ka maishe mu abin raini a wurin arna, Suna kaɗa mana kai, suna raina mu.


Ayuba, maganarka marar ma'ana ce, Ka yi ta maganganu marasa hikima.”


“Ba wanda zai amsa dukan wannan surutu? Yawan magana yakan sa mutum ya zama daidai?


“A cikin irin wannan wahala Ina bukatar amintattun abokai, Ko da na rabu da Allah, ko ina tare da shi.


Da sai in ba ka shawara ta ƙarfafawa, In yi ta yi maka maganar ta'azantarwa.


Ubangiji ya ce, “Birnin Urushalima yana yi maka dariya, kai Sennakerib, yana kuma yi maka ba'a.


Kin yi wa mutanen Isra'ila dariya. A kowane lokacin da kika ambaci sunansu, sai ki taɗa kanki da raini kamar an kama su tare da ɓarayi.


Suka ce, “Ka dogara ga Ubangiji, Me ya sa bai cece ka ba? Idan Ubangiji na sonka, Don me bai taimake ka ba?”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ