Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 16:13 - Littafi Mai Tsarki

13 Ya harbe ni da kibau daga kowane gefe. Kiban sun ratsa jikina sun yi mini rauni, Duk da haka bai nuna tausayi ba!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 16:13
16 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kibiya za ta kafe a jikinsa Tsininta zai yi ta ɗiɗɗiga da jini, Razana ta kama zuciyarsa.


Allah Maɗaukaki ya harbe ni da kibau, Dafinsu kuwa ya ratsa jikina. Allah ya jera mini abubuwa masu banrazana.


Idanuna sun dushe saboda kuka, Raina yana cikin damuwa. Zuciyata ta karai saboda halakar mutanena, Gama 'yan yara da masu shan mama Sun suma a titunan birnin.


tun da yake bai rangwanta wa mutanen tun can dā dā kuma ba, amma ya kiyaye Nuhu mai wa'azin adalci, da waɗansu mutum bakwai, sa'ad da ya aiko da Ruwan Tsufana zuwa a cikin duniyar nan ta marasa bin Allah,


Shi da bai hana Ɗansa ba, sai ma ya ba da shi saboda mu duka, ashe, ba zai ba mu kome tare da shi hannu sake ba?


“‘Tun da yake kin ƙazantar da Haikalina mai tsarki da gumakanki da abubuwanki masu banƙyama, hakika, ni Ubangiji Allah, zan kawar da ke, ba zan ji tausayinki ba, ba kuwa zan haƙura ba.


Zan gan shi ido da ido, Ba kuwa zai zama baƙo a gare ni ba. “Zuciyata ta karai saboda ku mutane kun ce,


Da na san zai yi haka, da sai in yi tsalle don murna, Da ba zan kula da tsananin azabar da nake ciki ba. Ban taɓa yin gāba da umarnan Allah ba.


Ubangiji ba zai gafarce shi ba, amma fushin Ubangiji da kishinsa za su auko a kan wannan mutum, dukan la'anar kuma da aka rubuta a littafin nan za ta bi ta kansa, Ubangiji kuma zai shafe sunansa daga duniya.


Maharba suka tasar masa ba tausayi Suka fafare shi da kwari da baka.


Ya aiko da rundunar sojansa don ta fāɗa mini, Suka haƙa ramummuka kewaye da alfarwata inda za su yi kwanto.


Akwai wanda zai iya ƙidaya mala'ikun da suke masa hidima? Akwai wurin da hasken Allah bai haskaka ba?


Ya ja bakansa kamar abokan gāba, Ya kuma nuna ikonsa kamar maƙiyi. Ya hallaka dukan abin da yake da bansha'awa. A alfarwar Sihiyona, ya zubo da hasalarsa kamar wuta.


Ya bauɗar da ni daga hanyata, ya yayyage ni, Ya maishe ni, ba ni a kowa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ